Nijeriya ta kudiri aniyar daukar likitoci daga kasashen Turai da Amurka don inganta bangaren lafiya, kamar yadda ministan lafiya na kasar Osagie Ehanire ya bayyana, a daidai lokacin da dimbin kwararru a fannin lafiya na kasar ke aiki a kasashen waje.
Wannan sanarwar ta ma’aikatar lafiyar Tarayyar Nijeriya na zuwa ne a daidai lokacin da masu ruwa da tsaki a bangaren ke bayyana takaici dangane da yadda ma’aikatan lafiya ke yin kaura daga kasar.
Osagie Enahire ya ce tuni jami’an ma’aikatarsa suka fara tattaunawa da ofisoshin Jakadancin kasashen waje da ke kasar, don zakulo kwararru da za su yi aiki a fannonin lafiya daban-daban a fadin Nijeriya.
Ministan ya kara da cewa ma’aikatar za ta bukaci karin kudade don samar da yanayin da zai kwadaita wa kwararrun likitoci ‘yan kasar da ke kasashen waje dawowa gida don tallafawa.
A shekarar 2018, wasu alkalumma sun nuna cewa kwararrun likitoci ‘yan Nijeriya, da ma’aikatan jinya sama da dubu 5 ne ke aiki da bangaren lafiya na gwamantin Birtaniya kawai.