• About Us
  • Blog
  • Gwamnatin Jihar Kano ta ce ana gabda fara ginin masana’antun Iskar Gas a Jihar
  • Home
Monday, March 20, 2023
  • Login
Dimokuradiyya
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
No Result
View All Result
Dimokuradiyya
No Result
View All Result
Home Labarai

Za Mu Inganta Lafiyar Al’umma Ta Hanyar Hana Bahaya Barkatai -UNICEF

Mustapha Haruna Dabai by Mustapha Haruna Dabai
June 9, 2019
in Labarai
Reading Time: 4 mins read
0 0
0
0
SHARES
4
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Garin Yammawar Kafawa da Jedawan Fulani garuruwa ne da ke yankin Karamar Hukumar Dambatta a jihar Kano da suka yi fama da cututtuka irin na amai da gudawa da Kwalara da sauran su a baya sakamakon rashin Bandakai da ya sa suke bahaya barkatai a fili.

Ganin ya sa Asusun Kula da Tallafawa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya bullo da wani shiri na WASH wato (Water Sanitation and Hygiene) da suke yaki da tsabtar Masai.

Shirin ya isa wadannan garuruwa biyu a yankin karamar hukumar ta Dambatta, inda al’ummar garuruwan suka yaba da wannan shiri sakamakon da basu san muhimmancin yin bahaya a shadda ba sai a fili sai da UNICEF ta shigo.

Yawan bahaya a fili ba a shadda ba hakan ne yasa asusun kula kananan Yaran na UNICEF yace a Najeriya akwai kimanin mutane Miliyan arba’in da bakwai (47) da basu da matsugunni suke bahaya a fili.

Ganin shirin na WASH da asusun kula da kananan Yaran ya isa garuruwan na Yammawar Kafawa da Jedawa a karamar hukumar Dambatta, wakilin mu ya ziyarci Yammawar Kafawa inda ya tattauna da al’ummar garin.

Tawagar UNICEF ta kai ziyarar fadar Hakimin Dambatta, Dokta Mukthar Adnan wanda har ila yau shi ne Sarkin Bai na jihar Kano, da ya godewa tawagar bisa ziyarar da suka kai dan duba yadda shirin wanke hannu da hana bahaya barkatai a fili idan anyi bahaya yake gudana.

Hakimin Dambatta, ya yi Magana ne ta bakin Ado Mukthar Adnan, yace suna godiya ga asusun kula da kananan Yara na UNICEF na yadda aka zabi karamar hukumar Dambatta, wajen hana yin bahaya barkatai.

Yace a karamar hukumar Dambatta gaba daya an rungumi wannan shirin domin da a can baya ana yin bahaya barkatai a fili wanda yasa jama’ar garin suke yawan kamuwa da cututtuka daban daban amma yanzu zuwan shirin an samu sauki jama’a suna tona shadda a gidajen su kuma kamuwa da cutattuka ya yi sauki.

Sarkin ya kuma ce daga zuwan shirin ya umurci Dagatan sa da masu Unguwanni da cewa su bai wa shirin hadin kai dan kare lafiyar su.

Da yake magana a fadar kwararren jami’in watsa labarai na hukumar asusun kula da kananan Yaran ta UNICEF Rabi’u Musa, cewa ya yi zuwan su garin Dambatta da wannan shiri an samu nasara.

Rabi’u Musa, ya kuma ce nasarar da aka samu ne yasa suka zo dan ganin yadda jama’ar suke ci gaba da rugumar shirin dan kare lafiyar su da ta sauran al’umma domin a cewar sa yin kashi a fili ba abun da yake haifar wa sai yaduwar cututtuka.

Binta Abdullahi, Matar aure a garin Yammawar Kafawa, cewa tayi da basu san amfanin wannan shiri na idan suka yi bahaya su wanke hannu ba sai yanzu da aka kawo musu shirin kuma da shaddar su ba ruwan su da marfi sai da aka kawo musu aka gaya musu illar barin ta a bude.

Tace da saboda suna barin shaddan su a bude suna yawan kamuwa da cututtuka na amai da gudawa saboda idan kudaje suka taso daga shadda sai kan abincin su amma tunda suka fara rufewa suka samu sauki.

Binta Abdullahi, ta godewa Allah ta godewa hukumar kula da asusun kula da kananan Yaran na UNICEF na kawo musu wanna shirin game da samar musu da ruwan sha.

Muhammad Sani, daya daga cikin mai bai wa Dattawan garin Shawara yace kafin zuwan WASH basu da shadda Yaran su a bayan gidajen su suke bahaya a fili idan iska ta ta shi sai ta debo kashin zuwa cikin abincin su daga karshe sai cuta iri iri amma zuwan WASH yanzu an samu canji.

Muhammad Sani, ya kara da cewa kafin zuwan WASH ko ruwan sha basu da shi a wata tsohuwar rijiya mai nisan gaba goma sha biyar suke shan ruwa amma yanzu WASH ta tona musu rijiyar burtsatse.

Yace da suna yawan fama da amai da gudawa da kwalara amma yanzu sun samu ruwa tsabtatacce da muhalli mai tsabta.

A cewar Muhammad Sani, garin Yammawar Kafawa, akwai mutane da suka kai yawan dubu daya da dari biyar da saba’in da bakwai, amma ko Firamare da asibiti ba su da shi.

Yace tun da UNICEF ta kawo musu wannan shiri na WASH to suna rokon gwamnatin da ta samar musu da asibiti da Makaranta.

Dan jin ko wane irin kokari hukumomi suke yi akai Shugaban karamar hukumar Dambatta Alhaji Idris Haruna Zago, yace suna kokari kare hakkin al’umma domin duk wani shiri da hukumar kula da asusun Yara na UNICEF ta kawo musu basa wasa da shi.

Idris Haruna Zago, ya godewa UNICEF da gwamnatin jihar Kano na yadda suka yi hadaka wajen kawo shirin kiwon lafiya da tsabtar Masai dan kare lafiyar al’umma.

Yace shi kansa ya san yana kokari abunda yasa ma yake samun nasarori a tsakanin sauran shugabanin kananan hukumomi yan uwan sa saboda ayyukan ci gaba da yake yi.

Ya kuma kara da cewa al’ummar garin Dambatta, da sauran kauyukan dake garin sun karbi shirin sosai musamman ma wadannan kauyuka na Yammawar Kafawa da Jedawa.

Ita dai hukumar UNICEF ta kirkiro yaki da tsabtar Masai ne dan kare yaduwar cututtuka da kuma ganin an shawo kan matsalar yin bahaya barkatai a fili.

Previous Post

Norway ta lallasa Super Falcons da ci 3 da nema

Next Post

Bahaushe Da Inyamiri

Next Post

Bahaushe Da Inyamiri

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result
Arabic Arabic English English French French Hausa Hausa
  • Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    2455 shares
    Share 982 Tweet 614
  • Da Ɗumi-Ɗuminsa: Ƙazamin Rikici Ya Kaure Tsakanin Shugaban Ƙungiyar CAN Da Isa Ashiru Kudan

    1995 shares
    Share 798 Tweet 499
  • Sai na yi lalata da kai na kwanaki 4 babu ƙaƙƙautawa sannan zan taimaka maka, Wata mata ga saurayi

    1693 shares
    Share 677 Tweet 423
  • Ga Irinta Nan: Budurwa Ta Koka Bayan Saurayinta Ya Ƙi Amsar Cikin Da Ya Ɗirka Mata

    1365 shares
    Share 546 Tweet 341
  • CBN Ya Sake Fitar Da Sabbin Bayani Kan Dawo Da Tsofaffin Takardun Kudin Naira

    1592 shares
    Share 637 Tweet 398
Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

March 20, 2023
INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

March 20, 2023
PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu

PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu

March 20, 2023
Bayan Faduwa A Zaben Sake Darewa Kujerar Sanata Nnamani Ya Bar PDP

Bayan Faduwa A Zaben Sake Darewa Kujerar Sanata Nnamani Ya Bar PDP

March 20, 2023
Mohammed Ya Sake Lashe Zaben Gwamna Karo Na Biyu A jihar Bauchi

Mohammed Ya Sake Lashe Zaben Gwamna Karo Na Biyu A jihar Bauchi

March 20, 2023
Da Dumi-Dumi: Ɗan Takarar APC Ya Lashe Zaben Gwamnan Jihar Sakkwato

Da Dumi-Dumi: Ɗan Takarar APC Ya Lashe Zaben Gwamnan Jihar Sakkwato

March 20, 2023
Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe
Labarai

Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

March 20, 2023
INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato
Labarai

INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

March 20, 2023
PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu
Labarai

PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu

March 20, 2023
Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe

March 20, 2023
INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato

March 20, 2023
PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu

PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu

March 20, 2023

Twitter

Archives

Recent Posts

  • Gwamna Umahi Ya Kori Wasu Mataimakansa Sa’o’i 48 Bayan Kammala Zabe
  • INEC Ta Bayyana Wanda Ya Lashe Zaben Gwamna A Jihar Filato
  • PDP Ta Lashe Kujeru 28 Na Majalisar Dokoki, Yayin Da APC Ta Tsira Da Hudu

Quick Links

  • Tsaro
  • Siyasa
  • Labarai
  • Wasanni
  • Kasuwanci
  • Rikicin Duniya

Contact Us

info@dimokuradiyya.com.ng

0809 912 4425 +234 809 912 4425

No. 218 Mogadishu layout Kaduna City Center Ahmadu Bello way kaduna. Kaduna, Nigeria 800273

Copyright © 2022 Dimokuradiyya Media Services LTD.

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio

Copyright © 2022 Dimokuradiyya Media Services LTD.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In