Hukumar Yaƙi da cin hanci a Najeriya EFCC ta kaddamar da fara bincike wasu jam’iyyun siyasa 18 dangane da hada haɗar kudin da suke yi a kasar.
Wannan dai ya biyo bayan yadda wasu yan siyasa ke ta Tururuwar siyan Fom din tsayawa takara, akan makudan kudade.
Dama tun kafin yanzu jama’a da dama ke ta kiraye kirayen ganin Hukumar EFCC ta binciki samun masu siyan Fom din.
Haka zalika EFCC ta bukaci hukumar zabe data bata bayanan bankuna da sauran bayanan da suka shafi kudi na jam’iyyun siyasa.
EFCC ta kuma nemi daraktocin bankin Access da Polaris da su mika mata bayanan ajiya goma sha hudu mallakin jam’iyar APC da PDP da na wata kungiya dake da alaka da jam’iyar PDP.
Hakan na zuwa ne a yayin da jam’iyyar APC ke siyar da Fom din takarar shugaban kasa kan kudi Naira Miliyan 100.