Gwamna Mai Mala Buni na Jihar Yobe da Hope Uzodinma na Imo Juma’a ne suka jagoranci wasu Sanatoci wajen mayar da fom din takarar Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmed Lawan.
An mika fom din ne a sakatariyar jam’iyyar APC mai mulki ta kasa dake Babban Birnin tarayya Abuja.
Da yake jawabi ga manema labarai, gwamnan Imo ya ce; “Kamar yadda kuka sani yawancin mu a nan ‘yan majalisar tarayya ne, Musamman kamar ni na bar majalisar dattawa a ranar Asabar don in je in yi zabe a jihar Imo kuma ina kan matsayina na gwamna a jihar Imo. A yau muna nan tare da hadin kai domin raka shugabanmu shugaban majalisar dattawa domin mika fom dinsa da ya kammala kuma mun mika fom din”.
Akan dalilin da ya sa yake ganin Shugaban Majalisar Dattawa shi ne ya fi dacewa da wannan aiki na shugabancin Najeriya Uzodinma ya ce; “A cikin ‘yan sanda, ana kiran irin wannan lamari esprit de corps”. “Ma’ana duk mu ne”.
A wani labari Kuma na daban.
Najeriya na da yara miliyan 18.5 d ba sa zuwa makaranta——UNICEF
Asusun talafawa yara na majalisar Dinkin Duniya yace yara fiye da miliyan goma sha takwas ne basa zuwa makaranta, inda fiye da Rabin adadin yara mata ne.
Wannan dai ba karamin lamari bane ga Nijeriya kasar da tafi kowace ƙasa yawan al’umma a nahiyar Afirka.
Shugabar ofishin UNICEF dake Kano Rahama Farah ne ya fadawa manema labarai cewa a kwai yara miliyan 18 da dubu dari biyar da basa zuwa makaranta, in da ya ce yara mata sun kai kashi 60 cikin dari na adadin.
Ya kara da cewa hare haren da yan ta’adda da sauran masu aikata laifukka da masu sace mutane domin neman kudin fansa ke kaiwa a makarantu yayi tasiri sosai wurin ƙaruwar lamarin.
Tun bayan da kungiyar boko haram ta sace mata yan makarantar sakandare a garin Chibok a jihar Borno da ke arewa maso gabas su fiye da 200 ake cigaba da samun irin makamancinsa a wasu makarantu da ke wasu yankunan kasar nan.
A shekarar bara yan bindiga sun sace a ƙalla yara yan makaranta fiye da dubu goma shabiyar (15000) inda aka tabbatar da mutuwar dalibai 16, kamar yadda UNICEF ya tabbatar.
Rahotan ya kara da cewa an saki wasu da aka kama bayan biyan cimma wasu yarjejeniya, yayin har yanzu ake cigaba da tsare wasu a cikin gandun daji.
UNICEF ta kara da cewa fiye da makarantu dubu goma sha day(11,000) a ka rufe saboda matsalar tsaro a Nijeriya tun watan Disambar shekara 2020, zuwa yanzu. Kuma a halin yanzu iyayen najin tsoron sanya ya yansu makarantu.
Bisa kara samun rufe makarantun da ake yi a Nijeriya , UNICEF yayi gar gadi akan yawaitar Auren wuri .
Jami’in na UNICEF ya ce a jihohin arewacin Najeriya cikin ko wadanni yara mata huɗu, ɗaya ce kawai ake iya samu wanda ta kammala karamar sakandare a yankunan karkara.