Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso, a ranar Juma’a, ya ce bai yanke shawarar akan zaben shugaban kasa na 2023 ba.
Kwankwaso ya kuma ce gwamnonin jihohi ba za su iya zama a Legas ko kuma a ko’ina a Arewacin kasar nan ba, don yanke shawarar shiyyar da za ta samar da shugaban kasa.
Ya ce kamata ya yi jam’iyyun siyasa su dauki matakin bayan an yi la’akari da duk wani abin da zai canza, ya ce abin da ke da muhimmanci shi ne a samu wanda ya dace ya yi aikin.
Tsohon gwamnan ya bayyana haka ne a wata hira da aka yi da shi a gidan Talabijin na Arise, inda ya kuma Bayyana wasu Lam’a a gwamnatin Gwamna mai ci Abdullahi Ganduje, inda ya ce bai gamsu da ayyukansa ba.
Ya soki bashin da jihar ke bi, inda ya ce a halin yanzu, a na bin Kano bashin Naira biliyan 187, wanda ba za a amince da shi ba.
Da aka tambaye shi ko zai tsaya takarar shugaban kasa a 2023, sai ya ce, “Ban dauki wannan matakin ba tukuna.” Inji Kwakwaso.