Yayin da zaben 2023 ke gabatowa, Babban Fasto na Cibiyar Bishara ta Duniya ta Dunamis, Paul Enenche ya yi gargadi game da magudi a zaben dake ta fe
Enenche ya bayyana cewa magudin zabe ba zai yi aiki ba a halin da Najeriya ke ciki.
Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake hudubarsa a hedikwatar cocin, Glory Dome da ke Abuja a daren jiya Laraba.
Limamin ya kuma bukaci jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC da su bijirewa yunkurin magudin sakamakon zabe mai zuwa.
Zaben 2023: Aregbesola Na Yi Mana Zagon Kasa A Jihar Osun —-Jam’iyar APC
A cewar Enenche: “Babu wani tsari na shaidan da magudi da zai yi aiki a wannan lokaci da muke ciki.
“Babu tsarin cin hanci da rashawa da zai yi aiki. Muna matsawa zuwa wancan gefen kuma babu abin da zai iya hana shi.
“Ya kamata mutane su dage su yi abin da ya dace, idan kana aiki a INEC ka yi abin da ya dace.
“Idan kafofin watsa labarun sashenku ne, kada ku ƙyale mutane su ba ku kuɗi don tura bayanan da ba da ce ba.