Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, Farfesa Yakubu Mahmood ya karyata wani rahoto da ke cewa zai iya sayen fam miliyan 100 na tsayawa takarar shugaban kasa a inuwar jam’iyyar All Progressives Congress wato (APC).
Wata sanarwa da babban sakataren yada labaran sa, Rotimi Yekanmi ya fitar, ta ce Yakubu ya kasance alkali mai kishin kasa wajen tabbatar da sahihin zabe.
Jaridar DAILY POST ta rahoto cewa Kungiyar Marubuta Kare Hakkokin Dan Adam ta Najeriya, HURIWA, ta bayyana cewa ba abin mamaki ba ne idan Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ya sayi tikitin takarar shugaban kasa na Naira miliyan 100, biyo bayan matakin da Gwamnan Babban Bankin Najeriya CBN Godwin Emefiele ya dauka na siyan Fom din.
Sai dai da yake mayar da martani, Yakubu ya ce wannan lamari ne da ba zai faru ba.
“An jawo hankalinmu kan wasu bata-gari a wasu wurare da bai kamata ‘yan Najeriya su yi mamaki ba idan Shugaban INEC ya shiga takarar Shugaban kasa ko ya bukace shi da ya yi hakan. Shawara ce ta rashin gaskiya. Kuma Hakan Ba zai faru ba.
“Shugaban ya kasance alkali mai kishin kasa wajen gudanar da sahihin zabe na gaskiya da adalci a fadin najeriya.
“Ayyukan da kundin tsarin mulki ya ba shi a matsayinsa na Babban Kwamishinan Zabe na Tarayya da kuma Jami’in kula da zaben shugaban kasa sun yi masa yawa har ya kai ga yin la’akari da bijirewa wasu abubuwa da suka saba wa doka, da’a da ka’idojinsa.
“Shugaban zai ci gaba da sauke nauyin da ya rataya a wuyansa ba tare da nuna fifiko ba, ko mugun nufi ga kowace jam’iyya ko dan takara ba.