A wani lamari da za a iya daukarsa a matsayin ba kasafai ba a fagen siyasa, daya daga cikin abokan takarar Farfesa Chukwuma Soludo ne ya zabe shi a zaben cike gurbi da ake yi a karamar hukumar Ihiala ta jihar Anambra.
Akachukwu Nwankpo, dan takarar gwamna na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), ya ce ya kada kuri’arsa ne ga abokin takararsa na jam’iyyar All Progressives Grand Alliance (APGA) a zaben.
Ya bayyana hakan ne ga manema labarai bayan ya kada kuri’arsa a yau Talata.
Karamar hukumar Ihiala ce tasanya hukumar INEC yanke hukunci a zaben da aka ayyana ba a kammala ba a ranar Litinin.
KARANTA WANNAN LABARIN: Anyi Bata kashi tsakanin Yan sanda da Yan Kungiyar IPOB a Ihiala
Soludo yana kan gaba da tazara mai nisan gaske a sakamakon kananan hukumomi 18 da aka bayyana.
A wani Labarin Kuma na daban.
Hukumar Kwallon Kafa Na Faransa Ta Tabbatar Da Raunin Pogba
Hukumar kwallon kafa ta Faransa ta ce dan wasan tsakiyar Manchester United Paul Pogba ba zai buga wasan neman cancantar shiga gasar cin kofin duniya da Faransa za ta yi ba saboda raunin da ya samu a cinyarsa a ranar Litinin.
Dan wasan mai shekaru 28 ya fice daga horo a sansanin Clairefontaine na Faransa bayan ya hi rauni.
Kungiyar Ole Gunnar Solskjaer ta Man United za ta buga wasa a ranar 20 ga Nuwamba da Watford a gasar Premier.
Hukumar FFF ta ce Pogba ya kasance “wanda ya ji rauni a cinyarsa ta dama”.
A ranar Asabar ne Faransa za ta karbi bakuncin Kazakhstan, inda take saran nasara, domin ta tabbatar da samun gurbi a gasar cin kofin duniya na badi, kafin wasansu na karshe na rukunin D a Finland mako mai zuwa.
Dan wasan tsakiya na Roma Jordan Veretout ne ya maye gurbin Pogba a cikin tawagar na Faransa.