Rundunar tsaro ta Civil defence ta sanar da aikewa da dakarunta dubu 20 jihar Anambra, gabanin zaben gwamnan jihar wanda aka tsara gudanar da shi ranar 6 ga watan Nuwamba mai kamawa.
Jihar Anambra dai cike take da kalubale na tsaro, wanda hakan ya sanya da dama ke kiran da a dage zaben, amma gwamnatin tarayya da hukumar zabe ta INEC suka jaddada cewa baza su dage zaben ba.
Dakarun rundunar daga bangarori daban daban aka aike da su zuwa jihar, da nufin kwantar da duk wani rikici da ka iya tashi kafin, yayin, da bayan kammala zaben.
Babban kwamandan rundunar Dr Ahmed Audi ne ya sanar da hakan yau Alhamis a Abuja, yayin da yake gabatar da jawabi a wajen wani taron bayar da horo na musamman kan gudanar da zabe, gabanin zaben jihar Anambra. Inda yace baki daya jami’an an dauko su ne daga yankin kudu maso kudu, da kudu maso gabas domin hallara a jihar ta Anambra.