A cikin wani sabon rahoto da hukumar zaben zaben kasar, Kenya ta fitar ta bayyana cewa zuwa tsakar rana, mutane miliyan shida da digo biyar 6.5 ne za su kada kuri’a a zaben kasar.
A cewar alkalan zaben kasar, wannan adadi da aka ambata ya kai sama da kashi 30% na wadanda suka yi rajistan zabe. Za a ci gaba da bude rumfunan zabe har zuwa karfe biyar na yammacin agogon kasar.
Rahotanni daga sassa daban-daban na kasar sun nuna cewa kawo yanzu ba a samu fitowar jama’a ba, idan aka kwatanta da zabukan da suka gabata a baya.
Hukumar ta yi ƙoƙarin magance matsalolin dake tattare da na’urar dake tantance yatsu kowani dan’adam, da aka ruwaito ana aiki da shi a wurare daban-daban da ake gudanar da zaben.
Shugaban Ƙaramar Hukuma Ya Kafa Dokar ta ɓaci a Karu, Jahar Nasarawa
A wani labarin kuma na daban.
Oluwo na Iwo, Oba Abdulrosheed Adewale Akanbi, ya bayyana Bola Ahmed Tinubu, na jam’iyyar APC a matsayin mafita ga kalubalen Najeriya.
Ya kuma bayyana Tinubu a matsayin wanda ya hada kai da ayyukansa suka yi tasiri wajen wada Najeriya wuri guda.
A wata sanarwa mai dauke da sa hannun Alli Ibraheem, babban sakataren yada labaransa, Oba Akanbi ya bayyana cewa a matsayinsa na dan Najeriya, Tinubu ya mayar da jihar Legas ta zama abin koyi ga sauran Jihohin kasar.
A cewarsa, “Tinubu dan Najeriya ne da aka wulakanta shi. Irin nasarorin da ya samu wajen mayar da jihar Legas tamkar wani katafaren ido, abin yabo ne matuka, Amanar Najeriya a hannunsa yakamata ya zauna, Za ku ga abin mamaki idan aka bashi dama”
Yayin da yake rokon wadanda suka yi Allah wadai da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Oluwo ya kara da cewa mulki ba shi da alaka da shekaru.
“Yawancin wadanda ke kalubalantar Tinubu na da al’amuran kashin kansu. Mutane da yawa suna cewa yana da girman kai domin yana faɗin gaskiya.
“Mutane suna iya tunanin shi mai girman kai ne domin yana faɗin gaskiya. Duk wanda ya fadi gaskiya an shar’anta shi da girman kai. Mutane suna cewa ni ma mai girman kai ne. Domin ina ƙaunar gaskiya kuma ina fadin ta.
“A ba shi Najeriya ya yi mulki ya rike, Zai yi abun al’ajabi kafin ka wani lokaci,” in ji shi