Shugaban Jam’iyyar NNPP Farfesa Rufai Ahmed Alƙali yace Jam’iyyar zata bada mamaki ga waɗanda suke ganin ita ba komai bace ba.
Ya bayyana haka a ranar Asabar a lokacin da yake jawabi ga Ƙafafen Yaɗa Labaru a Sakatariyar Jam’iyar dake Abuja.
Alkali yace Shuwagabancin Jam’iyyar tuni ta fara bin hanyoyi inganta Jam’iyyar NNPP na ganin ta inganta Siyasa ta hanyar baiwa ƴan Najeriya zaɓi na ƙarshe da zasu shigo domin ceto Najeriya daga hannun tsofaffin ruɓaɓɓun ƴan siyasa da basu da wata manufa mai kyau ga Ƙasar.
KARANTA WANNAN LABARIN: Dalilan da suka sanya na Janye daga Takarar Gwamna — Malami
A lokacin Zaɓen Fidda Gwani, yace Jam’iyyar ta fara bin hanyoyi domin zaɓar ƴan Takarar da zasu wakilci Jam’iyyar a shekarar 2023, yana mai cewa “wannan zai fara ne daga ranar Litinin 16 ga watan Mayu na Shekarar 2022 tare da tantance Ƴan Majalisun Jahohi zuwa ƴan Takarar Shugaban Ƙasa a Abuja a ranar 2 ga watan yunin Shekarar 2022”.
Yace Jam’iyyar zata bi dukkanin matakai domin ganin ta magance duk wani rikici a zaɓen fidda Gwani mai zuwa.
“Idan muka hau mulki da yardar Allah, zamu magance matsalar tsaro, dawo da darajar Naira, samar da Ayyukan yi ga Miliyoyin ƴan Najeriya, baiwa mata muƙamai a matakin Tarayya, gyara ma’aikatun da suka lalace, na saka da kuma inganta sana’o’i, da kuma mutunta Dokar Ƙasa da mutunta Dan Adam musamman yanda yake a Kundin Tsarin Mulki.
Comments 1