Gwamnan Zamfara, Bello Matawalle ya ce za su bai wa Fulani makiyaya damar karbar magani kyauta. Gwamnan ya ce sun dauki wannan matakin ne domin sun bunkasa walwalar Fulani a fadin jihar. Sannan ya ce wannan aikin na su wani mataki ne cikin na ayyukan da zai gabatar a cikin kwana 100 da kasancewa a karagar mulki.
Gwamnan ya shaida hakan ne a ranar Laraba a yayin kaddamar da shirin RUGA a Ranji Sakida dake Maradun a jihar. Alhaji Kabir Janyau, shugaban da ke jagorantar kwamitin lura da lafiyar, ya ce; za a yi hakan ne domin ganin an bunkasa walwalar makiyaya a jihar bisa tsare-tsaren gwamnati domin wanzar da zaman lafiya a jihar. Ya kara da cewa; suna sa ran dubban Fulani makiyaya ne za su amfana da wannan shirin wanda ya hada harda mata da kananan yara. Ya tabbatar da cewa; tuni suka hada tawaga wacce ke dauke da Likitoci da masu bada magunguna da likitocin jinya wato Nas domin gudanar da wannan aikin. Ya kara da cewa baya ga duba lafiyar Fulani makiyayan, za su kuma ba da magunguna kyauta ga dabbobin da suke kiwo.