Tsohon shugaban majalisar dattawa, Dakta Bukola Saraki, ya bayyana ziyarar da wasu gwamnonin jam’iyyar APC suka kai wa takwaran su na jihar Ribas, Nyesom Wike a matsayin aikin banza.
Gwamnonin jihohin Legas, Ekiti da Ondo, Babajide Sanwo-Olu, Dokta Kayode Fayemi da Olurotimi Akeredolu sun gana da Wike a Fatakwal a ranar Juma’a bayan ya dawo kasar daga Turkiyya, yayin da ake ta rade-radin sauya sheka daga jam’iyyar adawa.
Sai dai da yake zantawa da manema labarai jiya a Ilorin, Sanata Saraki ya ce ziyarar ba za ta zama komi ba a karshen ranar “saboda jam’iyyar PDP ba za ta bar Gwamna Wike ya tafi ba.
“Gwamna Wike muhimmin mamba ne a jam’iyyarmu, kuma ina da yakinin cewa nan da wani lokaci mai nisa za mu zauna mu magance dukkan matsalolin.
“Babu shakka cewa yana da dalilin jin yadda yake ji, amma akwai mafi kyawun hanyoyin da za a magance wannan batu.
“Abin da ke da kyau shi ne cewa duk muna magana da juna. Muna kan tattauna halin da ake ciki kuma PDP za ta sake haduwa kuma ta ci gaba don samun nasara a zabe mai zuwa,” inji shi.
A wani labari kuma na daban.
Ku ci gaba da sadaukar da rayuwarku domin zaman lafiyar Najeriya—–Farouk Yahaya Ga Sojoji
Shugaban hafsan sojin kasa (COAS), Laftanar Janar Farouk Yahaya, ya bukaci sojojin da ke yaki da masu tayar da kayar baya su kasance cikin shiri da kuma ci gaba da gudanar da rayuwar sadaukarwa domin shawo kan matsalar rashin tsaro da ke addabar kasar.
Janar Farouk, wanda shugaban tsare-tsare na rundunar, Manjo-Janar Andrew Omozoje, ya wakilce shi a ranar Asabar din da ta gabata yayin wani liyafar cin abincin rana ta hadin gwiwa da aka shirya wa sojoji a Maiduguri.
Ya kuma kara jaddada aniyarsa na inganta ayyukan jin dadin sojoji da iyalansu, musamman wadanda ke bukatar agajin gaggawa na kiwon lafiya, yana mai tabbatar da cewa za a ba su kulawa, a cikin gida da waje idan akwai bukatar hakan.
“Sallah ya ba mu dama ta musamman don yin tunani da kuma yi addu’a don neman yardar Allah Madaukakin Sarki Ya karya duk masu zagi da kuma kawo mana dawwamammen zaman lafiya a kasarmu. Ina roƙon ku da ku ci gaba da kasancewa da ƙwararrun ƙasar nan, da kishin ƙasa kuma ku kasance masu tsayuwa a cikin ruhi a duk lokacin da kuke bakin ayyukanku.
“Ina da sha’awar samar da ingantaccen aikin a fannin kiwon lafiya ga waɗanda suka sami rauni a fagen daga a cikin gida da waje, musamman don ba da tallafin ƙarfafawa don samun damar shiga cikin al’umma. Jindadin zai taimaka musu su shawo kan matsalolin da suka faru bayan rauni, ”in ji shi.
Anashi bangaren da yake jawabi Shugaban tsare-tsare na rundunar sojin saman Najeriya Air Vice Marshal Charles Ohwo, ya godewa dakarun bisa sadaukarwar da suka yi, ya kuma yi alkawarin cewa sojojin ba za su huta ba har sai an kawo karshen rashin tsaro fadin Najeriya.