Daga Khadija Mohammed Kano
Misali Kaine Kuna Soyayya da Budurwar ka tsawon Shekara 4 har an saka Muku Ranar Aure watarana taje Wajan wani Party kawai Sai Wani Sanata ya ganta yace yana so ya Aureta ita kuma tace Masa ansa Mata Rana Dan Allah yayi Hakuri.
shi kenan sai Sanatan yace Mata To Dan Allah Ba ni Lambar wanda za ki Aura, zan gaya masa wata magana.
Bayan ta bashi Lamba Sai wannan Sanata ya kira Saurayin nan nata Ya Gabatar Masa Da Kan sa kuma Yace, Dan Allah ina son ganin ka a Abuja.
Kuma in ba za ka damu ba ka Bani Lambar Bankin ka Zan turo maka kudin Jirgin Sama domin ka zo cikin Hanzari.
Bayan Ka Tura Masa da Lambar Kasa da Mintuna 15 sai ka ji Alert din Naira Miliyan 2 a Matsayin Kudin Jirgin Sama Kawai.
Kana Isowa Abuja yasa aka kawo ka Gidan Bakin sa bayan kun gaisa sai yace maka daman Akan Maganar Khadija ce Nake so ka barmun ita In Aureta Ni kamu zan baka Naira Miliyan 20 kaje ka Nemi wata Yarinyar ka Aura.