A karo na biyu jirgin Air Peace ya sake dauko wasu karin ’yan Nijeriya 319 daga Afrika ta Kudu, ya maido su gida Nijeriya.
An sauke su a Filin Jirgin Sama na Murtala Mohammed da ke Legas, daidai karfe 7:21 na dare.
Ma’aikatar Harkokin Wajen Nijieriya ta bayyana komai dangane da wadanda jirgin ya dawo da su. Kafin wadannan 319 dai an fara maido wasu 178, kuma dukkan su sun dawo ne don radin kan su. Kuma duk dai jirgin Air Peace ne ya dauko su.
Kafin isowar jirgin sai da Majalisar Tarayya ta gayyaci shugaban kamfanin jiragen Air Peace, Allen Onyema, inda ta gode masa tare da jinjina masa irin aikin jinkai tare da kishin Nijeriya da ya nuna, wajen dauko ‘yan Nijeriya kyauta daga Afrika ta Kudu.
Shugaban Majalisar Tarayya, Femi Gbajabiamila ya bayyana cewa tilas a yaba wa Onyema, domin ya sadaukar da ainihin harkarsa ta kasuwanci, ya maida jirginsa abin dauko jama’a kyauta ba tare da biyan ko sisi ba.
An gayyaci Onyema ne an yi masa wannan jinjina a lokacin da zauren majalisa ke cike makil.
Daga nan sai Gbaja ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta bai wa Onyema lambar yabo ta girmamawar nuna kishin kasar sa da ya yi.