An gurfanar da wasu mutane biyu Joseph Simon mai shekaru 25 da Oseni Meco mai shekaru 22 a ranar Talatar da ta gabata a gaban wata kotun Majistare da ke Ejigbo na jihar Legas.
Wadanda ake tuhumar, wadanda ba a bayyana adireshinsu ba, suna fuskantar shari’a kan tuhume-tuhume uku da suka hada da hada baki, sata da karbar kayayyakin sata.
Dan sanda mai shigar da kara, Insfecta Benedict Aigbokhan, ya shaida wa kotun cewa wadanda ake tuhumar da sauran su, sun aikata laifin ne a ranar 4 ga watan Afrilu da misalin karfe 3:30 na rana, a makarantar koyar da addinin islama ta Soundhope dake Baruwa na yankin Ipaja a jihar Legas.
Ya ce wanda ake kara na farko, Simon, ya saci na’urar sanyaya daki guda hudu, wanda kudinsa ya kai Naira 300,000, mallakar Soundhope International Muslim Academy.
Aigbokhan ya kuma ce wanda ake kara na biyu, Meco, ya karbi kadarorin, da sanin cewa an sace su ne.
A cewar sa, laifukan sun ci karo da sashe na 280(2) da 328 da 411 na dokar laifuka ta jihar Legas ta shekarar 2015.
Wadanda ake tuhumar dai, sun ki amsa laifin da ake tuhumar su da su.
Alkalin kotun, Mrs K.A. Ariyo, ya bayar da belin wadanda ake kara a kan kudi Naira 200,000 kowanne, tare da tsayayyu biyu kowannen su. Kuma ya dage ci gaba da shari’ar har zuwa ranar 10 ga watan Mayun shekarar 2022.
A wani labarin Kuma na daban.
Hukumar tsaro ta farin kaya NSCDC reshen jihar Zamfara ta tura jami’an rundunar sama da 700 zuwa cibiyoyin ibada da na shakatawa da dama a jihar Zamfara domin gudanar da bukukuwan Eidi karamar sallah da kuma hutun jama’a da gwamnatin tarayyar Najeriya ta ayyana.
A cewar kwamandan rundunar na jihar, Mista A A Sparks, wanda mataimakin kwamandan aiyuka, Mista B B Bodinga ya wakilta, yace rundunar ta tsara shirin ne domin tabbatar da an yi bikin Sallah babu kakkautawa, ba tare da samun wata damuwa ba a zukatar Al’umma.
Ya kara da cewa “Ba za a bar wani dutse ba wajen tabbatar da tsaro a jihar.”
Ya kuma gargadi duk ‘yan iska da masu shirya barna da su kaura daga jihar domin yanzu jihar Zamfara ba mafaka ce ta masu aikata laifi ba.
Kwamandan ta bakin Shugaban Ayyuka ya bayyana cewa, an yi wa rundunar gaggawar amsa tambayoyi tare da tura jami’ai yadda ya kamata domin fara sintiri kafin lokacin hutu da kuma bayan hutu.
Ya kuma ce dukkan wuraren shakatawa na motoci da tasha na bas daban-daban sun samu isassun hazikan jami’an hukumar domin duba zirga-zirgar ababen hawa.
“Rundunar ta kuma yi wani shiri na musamman a filayen idi daban-daban a lokutan Sallah domin daukar matakan tsaro.”
Sai dai kwamandan na jihar ya taya daukacin al’ummar musulmi murnar zagayowar watan azumin Ramadan da ke zuwa cikin nasara, sannan ya kuma yi musu fatan gudanar da bukukuwan karamar Sallah lafiya.