Sakataren Kungiyar masu fama da cutar sikila ta jihar Kano, Abdulkadir Muhammad, ya ce akalla mambobin kungiyarsu 80 ne suka mutu a shekarar 2019 saboda rashin jini, wanda matsin tattalin arziki ya haifar.
Sakataren, wanda ya yi hira da manema labarai a Kano, ya alakanta mutuwar mambobin ne da rashin jini da rashin kudin sayen magungunan da ya kamata su rika sha amma babu kudin saye.
A cewarshi, matsin tattalin arziki ya sa mafi yawan masu cutar basa iya zuwa asibiti saboda duba lafiyarsu akai-akai.