- Shugaban kungiyar likitoci ta duniya, Osahon Enabulele ya ce idan Najeriya tana son ta cika ka’idojin hukumar lafiya ta duniya na rabon likitoci tana bukatar guda 250,000
- Yanzu haka likitoci 50,000 ne kawai ke aiki a Najeriya
- Idan har Najeriya na son cika wannan gurbi dole ne ta sadaukar da kashi 15 na kasafin kudinta don samar da kiwon lafiya
Shugaban kungiyar likitoci ta duniya, Osahon Enabulele, a ranar Alhamis, ya ce idan Najeriya tana son ta cika ka’idojin hukumar lafiya ta duniya na rabon likitoci ga majinyata, kasar na bukatar likitocin da ba su gaza kasa da 250,000 a ma’aikatanta ba.
Osahon, wanda ya yi jawabi a matsayin bako mai jawabi a taron lacca da kungiyar Federated Chapel of the Edo Council wanda kungiyar ‘yan jaridu ta kasa NUJ ta shirya a birnin Benin, ya koka da cewa Najeriya na da likitoci kasa da 100,000, adadin da ya ce bai isa sosai ba don samar da rabon likitocin ga marasa lafiya.
KARANTA WANNAN: IGP Ya Bada Umarnin Gudanar da Cikakken Bincike Kan Farmakar Jami’in Dan Sanda
“Halin da ake ciki yanzu bisa ka’idojin kasa da kasa, yakamata a sanya likita guda ga marasa lafiya kasa da 600 amma a yanayin Najeriya, likita daya yakan duba sama da marasa lafiya 3,000.
“Don haka Najeriya na bukatar likitoci sama da 250,000 domin shawo kan lamarin a halin yanzu.
“Akwai kasa da likitoci 100,000 da suka yi rajista a Najeriya, an ce likitoci 98,000 ne bisa ga sabuntawar karshe.”
“A cikin wadannan likitoci guda 98,000, yanzu guda 50,000 ne kawai ke aiki a Najeriya,” in ji Enabile.
Shugaban na WMA ya jaddada cewa idan har Najeriya ta samu ingantaccen tsarin kiwon lafiya, dole ne a samu kudurin siyasa na shugabannin Najeriya na cimma yarjejeniyar Abuja na sadaukar da kashi 15 na kasafin kudinta don samar da kiwon lafiya.
Ya koka kan yadda shugabannin siyasa a kasar ke tafiya kasashen waje don yin layi kafin su ga likitoci marasa kwarewa don duba cutar hawan jini da za su iya yi a Najeriya yadda ya kamata.
Enabulele, ya bayyana rashin kudi, rashin isassun kayayyakin more rayuwa, rashin aikin yi, yanayin wurin aiki, albashi, tattalin arziki, hauhawar farashin kayayyaki da rashin ingantaccen kiwon lafiya da dai sauransu a matsayin matsalolin da ke fuskantar tsarin kiwon lafiyar Najeriya.
Ya ce dole ne gwamnatin Najeriya ta samar da ingantacciyar yanayin rayuwa ga mutane ciki har da kwararrun likitoci, yana mai cewa mutane da yawa suna son dawowa gida idan kasar ta gyaru.
“Akwai buƙatar kafa Hukumar Kula da Lafiyar Kiwon Lafiyar da za ta fi dacewa da tsarin kiwon lafiya da kuma fitar da ikon likita, horarwa, mafi kyawun albarkatun ɗan adam, haɓaka shirin da sauransu,” in ji shi.
A wani labarin kuma, EFCC ta Nada Sabon Kakakinta
Shugaban riko na hukumar EFCC, Abdulkarim Chukkol, ya nada fitaccen dan jarida, Dele Oyewale a matsayin kakakin hukumar
Sabon kakakin EFCC kafin na din nasa ya yi aiki tare da wasu kafafen yada labarai da dama
Ya samu lambobin yabo da dama bisa kwazon sa na aiki
Shugaban riko na hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC, Abdulkarim Chukkol, ya nada fitaccen dan jarida, Dele Oyewale a matsayin kakakin hukumar yaki da cin hanci da rashawar.
Jaridar PUNCH ta rawaito cewa nadin zai fara aiki nan take daga ranar Alhamis, 28 ga watan Satumba, 2023.