- Gwamnatin Imo ta kwace sama da kadarori 200 da gwamnatin tsohon Gwamna Rochas Okorocha ta mallaka a jihar
- Farfadowa da kuma dawo da martabar na daya daga cikin nasarorin da gwamna mai ci ya samu
- Gwamna mai ci ya gudanar da gagarumin aikin na gyara tare da gina jimillar tituna sama da 90 a jihar
Gwamnatin jihar Imo ta kwace sama da kadarori 200 da gwamnatin tsohon Gwamna Rochas Okorocha ta mallaka a jihar, Tribune Online ta rahoto.
Da take zantawa da manema labarai a ofishinta a ranar Alhamis, mai baiwa gwamna shawara ta musamman kan harkokin sadarwar, Chantel Chinyere Adanna Onwuzuruike ta bayyana cewa farfadowa da dawo da martabar na daya daga cikin nasarorin da gwamnan ya samu.
KARANTA WANNAN: Shugaban APC na Kasa Ganduje Ya Yaba da Hukuncin Kotun Koli Kan Tinubu
A cewarta daga cikin kadarorin da aka kwato wadanda ke da matukar muhimmanci a karkashin wannan shirin akwai kwato jami’ar Kingsley Ozumba Mbadiwe, Ogboko a karamar hukumar Ideator ta kudu dake Imo.
Ta ce jami’ar da aka gina kan sama da naira biliyan 40 na kudaden jihar, wani tsohon gwamnan jihar ne ya ware, inda ta ce gwamnatin ta kuma kwato wasu kasuwanni da aka gina da kudaden jihar a sassa daban-daban na jihar, amma an samu nasarar kwato wasu kasuwanni aka mika su ga makusantan gwamnatin da ta gabata.
Hadimar ta bayyana cewa Gwamna Hope Uzodinma ta kuma kwato takalman Imo a hannun AMCON tare da cire basukan Naira biliyan 1.6 da nufin bunkasa masana’antu da samar da ayyukan yi.
A cewarta, gwamnatin ta fara aikin gina babbar kasuwa ta zamani, wadda ke da shaguna sama da dubu uku, wadda za ta kunshi ofishin ‘yan sanda, bankuna, ofishin kashe gobara da sauran ababen more rayuwa da ayyuka da za a iya samu a cikin wata babbar kasuwar zamani
A bangaren noma kuwa, ta ce Gwamnan da hadin gwiwar NALDA sun sake gina gonar Acharaubo da ta lalace tare da farfado da rugujewar gonar Acharaubo a yankin Owerri ta Arewa tare da samun dimbin kwararrun manoma.
Mai bada shawarar ta ce bisa shawarar da kwamitin bincike na shari’a ya bayar, Gwamna Hope Uzodinma ya shiga aikin jajircewa na kwace duk wasu kadarorin da wasu gwamnatocin da suka gabata suka yi a bisa rashin adalci da kuma mayar da su ga wadanda suka mallaka.
A cewarta, rukunin gidaje na ‘Royal Palm Estate’ wanda aka gina tare da kudin masu biyan haraji, an gano shi tare da Shell Camp Quarters mai dauke da filaye kusan 50 da aka kwace ba bisa ka’ida ba daga hannun masu hannun jari aka sayar da su ko kuma aka baiwa ‘yan baranda.
A kan gyaran hanya, ta yi nuni da cewa, Gwamna yana da hanyoyin juyin-juya hali da za a iya karkasa su zuwa kashi uku, wato titunan sabunta birane, hanyoyin tattalin arziki da kuma hanyoyin shiga tsakani.
A cewar ta Uzodimma ya gudanar da gagarumin aikin na gyara tare da gina jimillar tituna sama da 90 inda ta kara da cewa wasu daga cikin wadannan an kammala su ne a yayin da sauran ke kan kammalawa daban-daban.
A wani labarin kuma, Lokaci Yayi Da Za A Yi Aiki Tare da Shugaba Tinubu – Omo-Agege Ga Atiku da Obi
Tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Ovie Omo-Agege, ya ce hukuncin da kotun koli ta yanke kan zaben shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kawo karshen cece-kucen siyasa
Atiku Abubakar da Peter Obi sun inganta harkar zabe tare da wadatar da hukunce-hukuncen Najeriya ta hanyar kararrakinsu na dimokradiyya
Ya kamata ‘yan siyasa si tashi tsaye wajen sake gina Nijeriya
Tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Ovie Omo-Agege, ya ce hukuncin da kotun koli ta yanke kan zaben shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kawo karshen cece-kucen siyasa da shugabanci.
Kotun kolin, a ranar Alhamis, ta tabbatar da hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke a baya.