- Gwamna Godwin Obaseki na jihar Edo ya ce Allah na gab da ceto Najeriya daga halin da ta ke ciki
- “Yana gab da sanya Najeriya tashi. Muna so mu gode wa Allah da abin da ya yi mana
- Duk da cewa abubuwa sun yi wuya a yanzu, za mu iya samun sauki da yardar Allah
Gwamna Godwin Obaseki na jihar Edo a ranar Lahadi ya ce Allah na gab da ceto Najeriya daga halin da ta ke ciki, Daily Post ta rawaito.
Gwamnan ya yi wannan jawabi ne a wani gangamin yakin neman zabe da Cocin Deeper Life ta shirya a birnin Benin, babban birnin jihar.
KARANTA WANNAN: Ministan Tinubu Ya Bayyana Lokacin Da Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki
Da yake lura da cewa Najeriya na shirin tashi, Obaseki ya ce, “Sun kawo mana Kiristi, sun kawo mana bege, sun kawo wani muhimmin sako wanda ya dace a wannan lokaci domin Allah yana gab da sako Najeriya domin Najeriya ta samu tashi.
“Yana gab da sanya Najeriya tashi. Muna so mu gode wa Allah da abin da ya yi mana a Jihar Edo. Muna so mu ci gaba da addu’a cewa duk da cewa abubuwa sun yi wuya a yanzu, za mu iya samun sauki kawai.”
Obaseki ya kuma nanata kudirin gwamnatin sa na ganin an samu zaman lafiya a jihar Edo.
Ya yi alkawarin cewa gwamnatin jihar za ta yi amfani da kudaden da take da su don amfanin al’ummar Edo baki daya.
“Duk abin da suke yi, ba za mu bar su su yi abin da suka saba yi a baya ba. Dole ne mu ba da bege ga matasanmu domin su ne makomarmu.
“Ina so in gode muku da kuka fito domin sauraron sakon mahaifinmu a wannan yakin na ‘yan Salibiyya. Duk duniya ta zuba mana ido, tana kallon Edo kuma da yardar Allah sakon da aka kawo ta wannan yaki zai ceci kasarmu kuma zai dawo mana da ci gaba.” Ya kara da cewa.
A wani labarin kuma, Shugaban LP Ya Kori Mataimakansa Biyar
Shugaban jam’iyyar Labour ta kasa, Julius Abure ya soke nadin mukamai biyar tare da fara aiki nan take
Akwai yiwuwar kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na Peter Obi zai ruguje nan ba da jimawa ba
Daga yanzu ku daina ci gaba da nuna kanku ga jama’a wajen ikirarin cewa ku mataimaka ne ga shugaban jam’iyya na kasa
Shugaban jam’iyyar Labour ta kasa, Julius Abure, a ranar Asabar, ya soke nadin mukamai biyar tare da fara aiki nan take.
Wannan lamari dai na zuwa ne a daidai lokacin da kotun koli ta yanke hukuncin da ya kawo karshen cece-kucen da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi da takwaransa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar suka yi na tsawon kwanaki 171 na soke zaben shugaban kasa Bola Tinubu.