- A wannan makon ne Shugaba Bola Tinubu zai tashi daga Abuja zuwa Riyadh, babban birnin kasar Saudiyya domin halartar taron Saudiyya da Afirka
- Bayyanar Tinubu a wajen taron ya nuna sabbin matakai na hada kan kasashen Larabawa don jawo hankulan ‘yan kasuwa don Zuba jari ga Najeriya
- Shugaba Tinubu zai yi duk mai yiwuwa don farfado da tattalin arzikin Nijeriya, ta hanyar amfani da rawar da ya taka a wadannan muhimman taruka biyu
A wannan makon ne Shugaba Bola Tinubu zai tashi daga Abuja zuwa Riyadh, babban birnin kasar Saudiyya domin halartar taron Saudiyya da Afirka da kuma taron kasashen Larabawa da za a yi a ranakun 10 da 11 ga watan Nuwamba, 2023, bi da bi.
Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, Ajuri Ngelale, shi be wanda ya yiwa manema labarai karin haske a ranar Lahadi a fadar shugaban kasa ta Villa dake Abuja.
KARANTA WANNAN: Da Dumi-Dumi: An Dawo Da Zirga-Zirgar Jirage Yayin da FG Ta Bude Filin Jirgin Saman Ibadan
Ngelale ya bayyana cewa, bayyanar Tinubu a wajen taron ya nuna sabbin matakai na hada kan kasashen Larabawa don jawo hankulan ‘yan kasuwa da kari kai tsaye daga kasashen waje don Zuba jari ga Najeriya.
Ngelale ya ce, “Shugaba Bola Tinubu zai nufi birnin Riyadh na kasar Saudiyya domin halartar manyan tarukan biyu.
“Na farko shi ne taron kolin Saudiyya da Afirka, inda za a tattauna batutuwa da dama da suka shafi dangantakar tattalin arziki a tsakanin yankunan da suka shafi yaki da ta’addanci, muhalli, noma, da sauran bangarori da dama na hadin gwiwa.”
Ngelale ya bayyana cewa makasudin halartar Tinubu shi ne kara habaka harkokin kasuwanci da zuba jari tsakanin Masarautar Saudiyya da kuma nahiyar Afirka.
“Tabbas, Shugaba Tinubu yana da matukar sha’awar tabbatar da cewa Tarayyar Najeriya a cikin yanayin da nahiyar ke ciki ta samu damar yin amfani da damammaki da za a samu ta hanyar aiwatar da yarjejeniyar ciniki cikin ‘yanci ta nahiyar Afirka, inda za mu kasance don samun kasuwanci guda daya na ‘yan Afirka sama da biliyan daya.
“Abin da ake sa rai a cewar Hukumar Tattalin Arziki ta Majalisar Dinkin Duniya a Afirka shi ne, a shekarar 2050, da kasuwar mu a nan nahiyar za ta haura dala tiriliyan 29,” in ji mataimakin shugaban kasar.
Tinubu zai halarci taron kasashen Larabawa da Afirka da za a yi ranar 11 ga watan Nuwamba a matsayinsa na shugaban kungiyar ECOWAS.
Shigarsa, in ji Ngelale, zai kara dankon zumunci tsakanin kungiyar kasashen Larabawa da kungiyar Tarayyar Afirka.
Ya kara da cewa, “Wannan zai samar da hadin kai ta fuskar samar da ababen more rayuwa, gudanarwa da kuma kafa sabuwar hanyar jirgin kasa mai sauri wadda za ta hada kasashen Larabawa daga Gabas ta Tsakiya da Arewacin Afirka, da sauran kasashen nahiyar.”
Da yake karkare jawabinsa, mai taimaka wa Shugaban kasar ya ce, “Ina so in tabbatar wa al’ummar Nijeriya a yau cewa Shugaba Bola Tinubu zai yi duk mai yiwuwa don farfado da tattalin arzikin Nijeriya, ta hanyar amfani da rawar da ya taka a wadannan muhimman tarukan guda biyu.
A wani labarin kuma, Kotun Daukaka Kara Ta Kori dan Majalisar Dattijai Mai Tsawatarwa Na Marasa Rinjaye
Kotun daukaka kara da ke zamanta a Legas ta kori dan majalisar dattijai mai tsawatarwa na marasa rinjaye Sanata Darlington Nwokocha daga majalisar
Kotun, a hukuncin da ta yanke, ta yi fatali da hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe ta Majalisar Dattawa ta yanke
Tuni jam’iyyar data yi nasara a kotun daukaka karar ta barke da murnar nasarar data samu
Kotun daukaka kara da ke zamanta a Legas ta kori dan majalisar dattijai mai tsawatarwa na marasa rinjaye Sanata Darlington Nwokocha daga majalisar.
Kotun daukaka kara ta kori Nwokocha, wanda ke wakiltar Abia ta tsakiya a zauren majalisar dattawa a karkashin jam’iyyar LP.