- Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Simon Lalong ya mika takardar murabus dinsa ga shugaban kasa Bola Tinubu a hukumance
- Ministan ya sauka daga wannan mukamin ne, domin samun damar zama a majalisar dattawa a matsayin Sanata
- A baya dai kotun daukaka kara ta bayyana shi a matsayin zababben dan majalisar dattawa bayan nada minista
Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Simon Lalong, a ranar Talata ya mika takardar murabus dinsa ga shugaban kasa Bola Tinubu a hukumance.
Lalong ya fice daga wannan aikin ne, domin samun damar zama a majalisar dattawa a matsayin Sanata mai wakiltar Filato ta Kudu Sanata.
KARANTA WANNAN: Rattaba Hannu Kan Kasafin Kudin 2024 Na N314bn Ya Zama Doka
An tabbatar da murabus din nasa ne a wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai taimakawa ministan mai barin gado ta fuskar yada labarai, Dr Makut Simon Maham ya fitar.
Ta bayyana cewa an mika wa Tinubu wasikar ne a ranar Talata, 19 ga watan Disamba, 2023.
Lalong ya bayyana cewa, bayan kammala shari’ar da aka kammala, kotun daukaka kara ta bayyana shi a matsayin zababben dan majalisar dattawa mai wakiltar mazabar Filato ta kudu tare da umurtar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta ba shi takardar shaidar cin zabe.
Ya kuma gode wa shugaban kasar da ya nada shi minista.
“Duk da haka, bayan tuntuba mai yawa, ya zama mai kyau a gare shi ya ci gaba da zama a Majalisar Dattawa ta 10 don ci gaba da ba da gudummawa ga ajandar sabunta bege na Shugaba,” in ji shi.
A wani labarin kuma, Insha Allahu Za a Kawo Karshen Rashin Tsaro A 2024, FG ta Sha Alwashi
Gwamnatin tarayya ta sha alwashin kawo karshen rashin tsaro a shekarar 2024
Ministan yace yana fatan matakin da Gwamnatin Tarayya ta dauka na hana tashe-tashen hankula zai taimaka wajen magance hare-haren ‘yan bindiga
Gwamnatin tarayya ta fahimci kalubalen tsaro da ke addabar al’ummar kasar nan
Gwamnatin tarayya ta sha alwashin kawo karshen rashin tsaro a shekarar 2024, inda ta kara da cewa ta fahimci kalubalen tsaro da ke addabar al’ummar kasar.
Karamin Ministan Tsaro, Dakta Bello Matawalle ne ya bayyana haka a wata hira da BBC Hausa.