- Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya Boss Mustapha, ya karyata rahoton da ke cewa yana da hannu wajen cire dala miliyan 6.3 daga babban bankin Najeriya CBN ba bisa ka’ida ba
- Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayyar ya ce ba shi da masaniya game da abin da ake cewa kan wannan Zargi na badakala
- Tsohon SGF ya yi kakkausar suka da kakkausar murya, inda ya ce zarge-zargen da ake yi ba su da tushe balle makama yaukuri ne na Karya da kuma kage
Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, SGF, Boss Mustapha, ya karyata rahoton da ke cewa yana da hannu wajen cire dala miliyan 6.3 daga babban bankin Najeriya CBN ba bisa ka’ida ba a lokacin gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Rahotanni sun bayyana cewa, wani mai bincike na musamman da shugaban kasa Bola Tinubu ya nada ya bankado wannan satar da ake zargin ta faru ne a ranar 8 ga watan Fabrairun 2023— makonni kafin zaben shugaban kasa.
KARANTA WANNAN: An Gwangwaje Mataimakin Shugaban Kasa Shettima, Ganduje da Mukaman Sarauta
Rahoton ya kuma yi zargin cewa Mustapha tare da tsohon gwamnan babban bankin kasa CBN Godwin Emefiele ne suka bayar da umarnin a cire kudaden da sunan bayar da tallafi ga tawagar sa ido kan zaben kasar waje.
Rahoton mai binciken ya ce faifan CCTV sun dauki yadda aka fitar da kudaden daga bankin na CBN.
Sai dai Mustapha a cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu tare da bayyana wa manema labarai a ranar Asabar, ya yi kakkausar suka da kakkausar murya, inda ya ce zarge-zargen da ake yi ba su da tushe balle makama.
Ya bayyana zargin a matsayin “kage karya” da kuma “yunkuri na kitsa” don kashe halinsa da kuma bata sunana.
Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayyar ya kara da cewa ba shi da masaniya game da abin da ake cewa “Uwargidan Shugaban kasa” da aka ambata a cikin rahoton a matsayin hujjar janyewar.
Ya yi nuni da cewa bai taba shiga cikin tattaunawa ko mu’amalar da ta shafi duk wani kudaden da ake biyan masu sa ido a zabukan kasashen waje ba.
Mustapha ya yi tambaya kan lokacin da za a gabatar da wannan zargi, yana mai nuni da fitowar ta a “lokacin Kirsimeti mai cike da damuwa” a matsayin wani abu da ke nuni da cewa da gangan wani yunƙuri ne na amfani da ra’ayin jama’a da shuka shakku.
Tsohon SGF ya yi kira da a gudanar da cikakken bincike na gaskiya kan lamarin, yana mai kira ga hukumomi da su “bincike tushen takardun da aka kirkira” tare da fallasa wadanda ke da hannu wajen yakin neman zabe.
Hakazalika ya yi kira ga jama’a da kafafen yada labarai da su yi tunani mai zurfi kuma kada su mika wuya ga rashin fahimta.
A wani labarin kuma, Kirsimeti: Gwamna Bala Ya Bai Wa Kiristoci Kyautar N120m
Gwamnan Bauchi Sanata Bala Abdulkadir Mohammed ya amince da gaggauta sakin zunzurutun kudi har Naira miliyan 120 domin siyan kayan abinci da sauran kayayyaki
Tuni gwamnan ya amince da sakin albashin watan Disamba ga ma’aikatan gwamnatin Jihar don taimaka musu wajen yin sayayya a wannan lokaci na kirsimeti
Masu bukatu na musamman da ke bukatar kulawa na daga cikin wadanda suka ci gajiyar wannan gagarumin karimci
A wani yunkuri na tabbatar da ganin al’ummar kiristoci a jihar Bauchi na gudanar da bukukuwan murnar zagayowar ranar kirsimeti, Gwamna Sanata Bala Abdulkadir Mohammed ya amince da gaggauta sakin zunzurutun kudi har Naira miliyan 120 domin siyan kayan abinci da sauran kayayyaki.
Za a raba kayayyakin ne ga dukkanin kungiyoyin kiristoci da ke karkashin inuwar kungiyar kiristoci ta Najeriya (CAN) domin gudanar da bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara ta 2024 cikin walwala a fadin jihar.