By Abbas Yakubu Yaura
An yi fargabar mutuwar mutum guda tare da jikkata wasu da dama a wata zanga-zangar da iyaye da dalibai musulmi suka yi kan hana amfani da hijabi da makarantar sakandare ta Oyun Baptist (OBHS) da ke Ijagbo ke ci gaba da yi, ta rikide zuwa tashin hankali a ranar Alhamis.
An tattaro cewa iyayen da daliban sun isa makarantar ne da misalin karfe 7 na safe don nuna rashin amincewarsu da matakin amma wasu ‘yan daba suka far musu.
A daya daga cikin faifan bidiyo da ke nuna yadda lamarin ya faru, an ga masu zanga-zangar sun yi kaca-kaca da harbin bindiga.
Wani mazaunin Ijagbo, Alhaji Soliju, ya ce an girke jami’an tsaro a kofar makarantar yayin da fasassun kwalabe suka cika kasa.
Wani mazaunin garin da ba ya so a buga sunansa ya shaida wa wakilinmu ta wayar tarho cewa an gudanar da zanga-zangar cikin lumana har aka kai harin.
Mazauna garin ya ce, “Musulman sun ci gaba da zanga-zangar a kofar makarantar da safiyar yau kafin wasu ‘yan daba su far musu.
“Na ga wani yaro da ya samu rauni a cikin lamarin an garzaya da shi asibiti a kan babur. Ba mu san ainihin ko an harbe shi ko kuma an yi kama da hakan ba, amma mun ji cewa daga baya ya mutu.
“Wani yaro kuma ya gamu da ajali a yayin da ‘yan baranda suka zo da adduna da bindigu, sannan wasu da dama sun jikkata. Muzaharar ta kasance cikin lumana har aka kai harin.”
Ya kara da cewa, “Ko da yake lamarin ya kwanta yanzu, amma ba mu san abin da zai iya faruwa ba.”
An tattaro cewa bankuna da sauran makarantun da ke kusa da wajen sun rufe sakamakon afkuwar lamarin.
Kiraye-kirayen da aka yi wa Sakataren kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) na jihar, Rev Timothy Reuben Ibitoye, bai amsa ba.
Kakakin ma’aikatar ilimi, Kamaldeen Aliagan, ya ce nan ba da dadewa ba za a fitar da sanarwa kan lamarin
Idan dai za a iya tunawa, kafin aukuwar lamarin kofar makarantar, dalibai da iyayen yara a ranar Laraba, sun mamaye gidan gwamnati da ke Ilorin, domin nuna rashin amincewarsu da matakin da OBHS ta dauka kan lamarin.
Wasu daga cikin iyayen sun shaida wa manema labarai cewa an hana su kwana a makarantar tun makonni uku da suka wuce duk da umarnin da gwamnati ta bayar na akasin haka.
Sun kuma zargi shugabancin kungiyar Kiristocin Najeriya reshen jihar kan lamarin.
Kafin wannan lokacin Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa gwamnatin jihar Kwara, a ranar Talata, 25 ga Janairu, 2022, ta sake jaddada manufofinta tare da ba da umarnin gudanar da makarantu a jihar da su ba da damar amfani da hijabi da huluna na mata ta hanyar dalibai wadanda suka da bukatar hakan.
Haka kuma, tawagar gwamnati karkashin jagorancin kwamishiniyar ilimi Hajiya Sa’adatu Modibbo Kawu, ta ziyarci makarantar sau biyu domin warware matsalar.