By Abbas Yakubu Yaura
Wasu daga cikin matan Gwamnonin kasar nan sun bi sahun kungiyoyin mata daban-daban da suka yi zanga-zangar nuna rashin adalci a kofar Majalisar Dokokin kasar a ranar Talata.
Wadanda suka shiga zanga-zangar sun hada da matar Gwamnan jihar Ekiti Erelu Bisi Fayemi, da Edo, Betty Obaseki da kuma jihar Akwa Ibom, Martha Udom.
Fayemi ce ta jagorance su, inda ta ce sun je filin zanga-zangar ne domin su tsaya wa dukkan matan Najeriya hadin kai.
“Mun zo nan ne domin neman hakkinmu. Muna son shugabanninmu a Majalisar Dokoki ta kasa su gane cewa matan Najeriya suna da matsala,” inji ta.
Misis Obaseki ta kuma bayar da tallafin ta ce duk wanda ya yi watsi da muradin mata zai fadi zabe a jihar Edo.
Misis Emmanuel, wacce ta jaddada ayyuka 35 na tabbatar da gaskiya ga mata, ta bukaci a baiwa mata damar ba da gudummawarsu ga ci gaban al’umma.
Ita ma shugabar hukumar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje (NIDCOM), Abike Dabiri, ta halarci wajen zanga-zangar.
Ta ce mata ba wai suna neman mafita ba sai dai neman adalci.
Wasu Sanatoci mata kuma sun shiga zanga-zangar, inda suka yi kira da a daidaita jinsin mata.