Ambaliyar a ranar Juma’a ta rushe gidaje 66 kuma ta sanya kusan mutane 2,000 sun rasa matsuguni a cikin Orsu Town a cikin Karamar Hukumar Oguta na jihar Imo.
Memba mai wakiltar mazabar Oguta a majalisar jihar, Frank Ugboma, wanda ya ziyarci yankin a jiya, ya yi kira da a sanya baki daga hukumomin da abin ya shafa don sake maido da mutanen da suka rasa muhallinsu tare da rage musu radadin halin da sukebciki.
Dan majalisar, wanda ya ziyarci yankin da ambaliyar ta bulla don tabbatar da matakin da ambaliyar ta lalata, wanda ya nuna nadama kan lamarin ya bukaci gwamnatin jihar Imo da ta bayar da taimako na gaggawa ga mutanen da rikicin ya ritsa da su.
Ya ce Oguta ya gamu da ambaliyar “Wannan yanki ne da nake wakilta a yankin namu ne yankin da ke fama da ambaliyar amma ina tabbatar wa mutanena cewa tabbas zan gabatar da wannan matsalar a farfajiyar gidan”, in ji shi.
Dan majalisar ya roki NEMA da ta sa baki a lamarin don kayan agaji da kuma sauran hanyoyin tallafawa wadanda ambaliyar ta shafa.
Shugaban ofishin ayyukan Imo / Abia na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta kasa, Evans Ugoh, ya yi kiran rushe gidaje da aka gina kan hanyoyin ruwa a yankin.