By Abbas Yakubu Yaura
Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Juma’a ta bayyana wasu mutane 12 da ake nema ruwa a jallo bisa aikata laifuka daban-daban a jihar Anambra.
Ana tuhumar wadanda ake zargin da hada baki, kisa, fashi da makami, ta’addanci, garkuwa da mutane, kungiyar asiri da kuma mallakar makamai ba bisa ka’ida ba.
Tsohon Shugaban Kasar Kenya, Mwai Kibaki, Ya Rasu Yana Da Shekaru 90
Wasu kuma nayin fashi da makami, da barna, da kuma dabi’ar da ka iya haifar da rashin zaman lafiya a Isu-Aniocha, karamar hukumar Awka ta Arewa.
Sunayen wadanda ake nema ruwa a jallo sun hada da Edward Okoye (aka Stone); Donatus Okeke; Onyemazi Ngini; Onyebuchi Nwekeizu Okoye; Nonso Eboh; Chukwuka Onyibor.
Sauran su ne, Chukwujekwu Anaekeokwu; Chuka Ilodigwe; Chinedu Nwoye Okoye; Nonso Awusionwu Obinna; Cosmos Okonkwo da Chukwujekwu Okoye.
Tun da farko dai rundunar ‘yan sandan ta samu umarnin kotu na bayyana cewa ana neman su, kamar yadda kakakin rundunar Muyiwa Adejobi ya bayyana.
Shekarunsu wadanda ake nema suna tsakanin shekaru 25 zuwa 55 kuma ‘yan asalin Isu-Aniocha ne; tsawon su yana tsakanin 1.5m zuwa 1.7m.
Edward Okoye, tare da wasu, ana zargin sun harbe wasu mutane biyu – Ifeanyi Anazoba (aka Ichafu) da Chukwuebuka Amodo (aka Mutum).
Lamarin ya faru ne a wani taron binne mutane a dakin taro na garin Umuzuocha da ke Awka ta Kudu a jihar Anambra a ranar 19 ga watan Janairun shekarar 2019.
An fille kawunan wadanda suka mutu tare da kona gawarwakinsu. bayan ganewa.
Ana kuma zargin Okoye da wasu da laifin yin garkuwa da mutane biyu tare da lalata kadarori biyu da kudinsu ya haura Naira biliyan 1.2.
Wadanda ake zargin sun kuma ‘kai hari tare da cin zarafin wasu jami’an ‘yan sandan wayar tafi da gidanka domin dawo da kwanciyar hankali a cikin al’umma.
Rundunar ‘yan sandan ta yi kira ga jama’a da su taimaka da bayanai masu amfani da za su saukaka kama su.