Bulaliyar Majalisar Dattawa, Sanata Orji Uzor Kalu, ya ce ba shi ne Darakta Janar na kungiyar yakin neman zaben Sanata Ahmed Lawan ba.
Sanata mai wakiltar Abia ta Arewa yana mayar da martani ne kan rahotannin da kafafen yada labarai suka bayar wanda ya sanya shi a matsayin Darakta Janar na kungiyar.
A wata sanarwa da Kalu ya aike wa manema labarai, ya ce, “Ya kamata a yi watsi da jerin sunayen, saboda ba a ba da izini ga shirin buga shi ba.”
Ya ce, “Yana da muhimmanci a sanar da jama’a cewa har yanzu ba mu shiga yakin neman zabe ba.
Za a kaddamar da wani kwamiti da zai tabbatar da hakan da zarar dan takarar da muka fi so, Sanata Ahmad Lawan ya fito a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC.”
Kalu ya kara da cewa, “Ni ma na fito takara a yankina na dan majalisar dattawa, kuma na gwammace gwamna mai ci wanda baya tsayawa takara ya jagoranci tawagar yakin neman zaben a lokacin da ya dace.”
A cewarsa, wasu maziyartan masu zaman kansu da ma ba a cikin taron ba an ruwaito sun halarci taron, ciki har da Sanata Betty Apiafi da Sanata Uche Ekwunife wadanda suka ziyarci wani taro na daban da ya shafi majalisar dattawa
Sanatan Ya yi gargadin cewa, “Bari a sanya wadannan sunayen a matsayin wani bangare na kungiyar yakin neman zaben Ahmad Lawan”.