Rundunar ‘yan sandan jihar Legas a jiya ta ce har yanzu ba ta ga wata kwakkwarar hujjar da ta nuna cewa an kai hari kan magoya bayan jam’iyyar Labour a Epe ba.
Wani tsohon kwamishina a tsohuwar gwamnatin gwamna Akinwunmi Ambode a Legas, Olawale Oluwo, ya ce ya tsallake rijiya da baya lokacin da aka ce an harbe shi a ranar Asabar.
KARANTA WANNAN LABARIN: Da Dumi-Duminsa: CBN Ya Umarci Bankuna Su Cigaba da Mu’amulla da Tsofaffin Naira – Wani Gwamna Ya Tabbatar
Ya ce lamarin ya faru ne a lokacin yakin neman zaben dan takarar gwamna na jam’iyyar Labour, Gbadebo Rhodes-Vivour, a karamar hukumar Epe.
Oluwo, dan takarar jam’iyyar Boot a zaben gwamna da za a yi a ranar 18 ga watan Maris, ya narke a kwanan baya cikin jam’iyyar LP.
Ya ce yana tare da jigo a jam’iyyar PDP, Noheem Balogun, wanda shi ne dan takarar majalisar wakilai ta tarayya na jam’iyyar adawa a Epe, da sauran jiga-jigan a yakin neman zaben.
Sai dai a zantawarsa da Daily Trust ta wayar tarho, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Benjamin Hundeyin, ya ce, duk da cewa an bayar da rahoton hakan a ranar Lahadi, amma bincike ya nuna cewa babu wata kwakkwarar hujja da ta nuna an kai harin.
Hundeyin ya ce jami’in ‘yan sandan shiyya na Epe ya ziyarci wurin domin gudanar da bincike a kan lamarin, amma bayan sa’o’i na bincike rundunar ba ta ga wata alama da ke nuna cewa an kai harin ba.
“’Yan sanda ba wai karya suke yi ba, amma kamar yadda aka gina fadar Shugaban kasa da Majalisar Dokoki ta kasa, mun ga bidiyon hare-hare da wadanda suka jikkata a shafukan sada zumunta.
“Babu irin wannan shaida lokacin da ‘yan sanda suka ziyarci wurin. Har yanzu dai ba mu ga wanda ya fito ya ce ya ji rauni a harin ba.
“Don haka a yanzu babu wata shaida da ta nuna irin wannan harin,” in ji shi.
Da yake magana kan harin na ranar Asabar a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Oluwo ya ce an kai harin ne a unguwar Ita Opo da ke Legas a lokacin yakin neman zaben LP.
Ya ce duk da harin, muzaharar ta yi nasara in ban da “ayyukan da wasu bata gari suka aikata, wadanda ake zargin an dauki nauyinsu ne daga wuraren da ba a yi tsammani ba, don haifar da tashin hankali da fargaba.”
“Gbadebo ya kasance a wurin, kasancewar shi ne gaba daya jagoran tawagar. Alhamdu lillah sun rasa daga inda aka kai musu hari amma godiya ta musamman ga jami’an tsaro na da suka mayar da martani nan take domin fatattakar maharan biyu Ana mika rahoto ga ‘yan sanda kan lamarin.”
Rhodes-Vivour ya kuma tabbatar da harin a shafin sa na Twitter da aka tabbatar a jiya, yana mai cewa, “Taron jiya ya yi kyau, mun hade kuma mun ga magoya baya a Epe. An kai mana hari amma duk muna cikin koshin lafiya.”
A wani labarin kuma, Mutane Dubu 48,000 Ne Girgizar Kasa Ta Hallaka A Turkiyya — Erdogan
Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdoğan ya bayyana cewa, adadin mutanen da girgizar kasar data afku a yankin Kudu maso Gabashin Turkiyya ta kashe ya kai dubu 48,000 tare da jikkata sama da dubu 115,000.
Erdogan ya bayyana hakan ne a wani jawabi da ya yi wa al’ummar kasar ta talabijin daga gundumar Samandag da ke lardin Hatay, inda ya ce, adadin wadanda suka mutu ya kai dubu 48,000, kuma wadanda suka jikkata ya zarce dubu 115,000.