Badakalar biliyan 44: EFCC ta garƙame asusun da NSIPA ta tura biliyan 30
Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta bincika tare da garƙame Naira biliyan 30 daga cikin Naira biliyan 44 da aka kwaso daga asusun Hukumar Kula da Zuba Jari ta Kasa, NSIPA.
Wannan ci gaban ya zo ne sa’o’i 24 bayan da Halima Shehu, mai kula da harkokin NSIPA ta kasa, EFCC ta tsare tare da kama ta bayan shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da ita.
KARANTA WANNAN LABARIN:Kotu Ta Daure Barawon Babur Watanni 12 A Abuja
Wata majiya da ba a bayyana sunanta ba ga jaridar The Nation ta bayyana a ranar Laraba cewa an garƙame asusun ajiyar da wasu jami’an NSIPA suka tura hukumar yaki da cin hanci da rashawa a ci gaba da bincike.
“Bayan an shafe sa’o’i ana bincike tare da bayyana wasu asusu da yawa, EFCC ta tabbatar da cewa an fitar da Naira biliyan 44 ba tare da izini ba daga asusun NSIPA zuwa wasu asusun sirri da na kamfanoni”.
A ranar Larabar da ta gabata ne EFCC ta kai karar Shehu kan zargin damfara.
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kuma kama tsohon Daraktan kudi da asusu na NSIPA, Bwai Adamu Hamza.
Hamza ta yi ritaya daga hukumar a watan Disamba.
A jiya ne wata tawaga ta musamman ta yi wa Shehu da Hamza tambayoyi.