Rahotanni sun bayyana cewa wakilan kungiyar kwallon kafa ta Barcelona na kasar Spain sun yi wata ganawar da ba a bayyana ba da mahaifin Lionel Messi kuma suna shirin baiwa wanda ya lashe kofin duniya bankwana da kungiyar a cewar Barca Blaugranes.
Messi ya bar Camp Nou zuwa Paris Saint Germain ta Faransa a lokacin bazara na shekarar 2021 amma ba a ba shi girma a kulob din da ya shafe mafi yawan rayuwarsa ba.
KARANTA WANNAN LABARIN: Jami’ar Jihar Kogi Ta Kori Wasu Ma’aikata Bakwai Bisa Zarginsu da Zambar Albashi
Kwantiraginsa na yanzu a PSG zai kare ne a bazara mai zuwa kuma wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or sau bakwai ya nuna rashin jin dadinsa a kungiyarsa ta yanzu kuma yana neman ya koma.
Bisa dukkan alamu dai batun taron shine tattauna batun komawar Messi Barcelona, har yanzu ana tattaunawa kan ko zai farfado ko a’a.
Wani dalili na ganawar shi ne don daidaita dangantakar da ke tsakanin dangin Messi da kulob din bayan dan uwan Lionel Matias ya kunyata kulob din a fili cewa ya zama “karamin kulob” kafin Messi ya shiga.
Idan dan wasan mai shekaru 35 bai koma Spaniya ba a matsayin dan wasa za a yi masa bankwana tare da bikin cika shekaru 125 na Barcelona wanda zai kasance kafin kakar wasa ta 2024/25.
An danganta dan wasan na Argentina da kungiyar MLS ta Inter Miami kuma da alama kungiyar Larabawa ta Al Halal SFC na tunanin daukar matakin, wanda zai iya sake farfado da kishiyar “GOAT’ tsakanin Lionel da Cristiano Ronaldo.
Ya kasance muhimmin abu ga dan wasan na Paris a wannan kakar inda ya zura kwallaye 11 kuma ya taimaka sau 10 a gasar Ligue daya, inda ya ci nasara a kan LOSC Lille a wasansu na karshe na gasar.
A wani labarin kuma, NBC Ta Yi Barazana Soke Lasisin Kafafen Watsa Labarai Kan Zafafa Kalaman Siyasa
Hukumar yada labarai ta kasa, NBC, a ranar Alhamis, ta yi barazanar soke lasisin duk wani gidan yada labarai da aka samu yana zafafa harkokin siyasa gabanin zabukan 2023, lokacin da kuma bayan babban zaben kasar.
Babban Daraktan NBC Balarabe Ilelah ne ya bayyana hakan a Kano a taron karawa juna sani na kwana daya da gwamnatin jihar Kano tare da hadin gwiwar hukumar suka shirya.