Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa Bola Tinubu, Femi Gbajabiamila, ya ce an tsara tsarin neman rancen dalibai ta hanyar da babu wata alaka tsakanin masu kula da lamuni da masu cin gajiyar shirin.
Gbajabiamila ya ce ana ci gaba da kokarin ganin an fara shirin a watan Janairun 2024 don tabbatar da cewa daliban Najeriya za su iya samun lamunin don samar da kudirin neman ilimi.
Karanta nanBa Zan Baiwa ‘Yan Jahar Kebbi Kunya Ba-Gwamna Nasir Idris
Ya yi wannan jawabi ne a Legas ranar Juma’a a lokacin da yake gabatar da lacca mai taken, “Karfafa Matasan Nijeriya Kan Tattalin Arzikin Yau” a wajen taro karo na 35 na Kwalejin Fasaha ta Yaba (YABATECH).
Gbajabiamila ya ce, domin kar a samu wata matsala,masu bukata za su yi amfani da yanar gizo, a tantance su ta hanyar yanar gizo, kuma za su yi la’akari da takardun shaida da suka gabatar.
Ya ce,babu wanda zai bukaci sanin kowa don ya cancanci wannan lamuni domin samun damar wannan tallafin ya zama daidai da gaskiya.
Kwanan nan, Tinubu ya rattaba hannu kan dokar ba da lamuni ga dalibai.
Bayan sanya hannu kan kudirin dokar, shugaban kasar ya ba da tabbacin cewa babu wani dalibi da zai fice daga makarantun gaba da sakandare saboda rashin iya biyan kudinsa.
Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta tabbatar da cewa cibiyoyin ilimi sun samu abubuwan da suka dace don gudanar da ayyukansu na harkar ilimi kama daga kayan aiki,albashi alawus alawus da sauransu.
A wani labarin kuma‘Yan Sanda Sun Gargadi Jam’iyun APC Da NNPP A Kano Akan Shirin Taron Gangami
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta fitar da wani sabon gargadi a kan jam’iyyar APC da kuma jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) da ke shirin gudanar da taron gangamin.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mista Hussaini Gumel ne ya bayyana haka a wata tattaunawa ta wayar tarho da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a ranar Juma’a a Kano.
Gumel ya bayyana cewa tuni rundunar ta fara sintiri sosai a cikin birnin da kewaye domin tabbatar da doka da oda