Biafra: Kotun Koli za ta yanke hukunci kan makomar Nnamdi Kanu a yau
Yanzu komai an shirya domin Kotun Koli ta yanke hukunci kan makomar jagoran masu fafutukar kafa kasar Biafra, IPOB, Nnamdi Kanu a yau Juma’a.
Kanu yana tsare tun watan Yunin 2021 lokacin da aka sake tsare shi a Kenya kuma aka dawo da shi a Najeriya.
KARANTA WANNAN LABARIN:Allah Ne Ya Aiko Mani Akpabio Domin In Yi Aiki Tare Dashi -Tinubu
Da dawowar sa, gwamnatin Najeriya ta gurfanar da shi a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja, bisa tuhume-tuhume hudu da suka hada da cin amanar kasa, da hada baki wajen aikata laifin cin amanar kasa, shigo da kayan rediyo ba bisa ka’ida ba, da kuma bata sunan tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Daga baya tsohon babban lauyan gwamnatin tarayya, Abubakar Malami ya janye tuhumar wanda ya maye gurbinsu da sabbin tuhume-tuhume 14 da suka shafi ta’addanci da kuma zama mambobin kungiyar da aka haramta.
Kotun ta rage tuhumar zuwa tuhume-tuhume bakwai da kotun daukaka kara ta soke.
Cikin rashin jin dadin hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke, gwamnatin Najeriya ta shigar da kara a kotun koli.
Da yake tsokaci game da hukuncin da ake sa ran za a yanke, wani mai fafutuka da zamantakewar al’umma a Abuja, Deji Adeyanju, ya ce ya kamata kotun koli ta bayar da Kanu beli.
Ya ce: “Fata na ita ce Kotun Koli ta yanke hukuncin da kowa zai yarda da shi, amma ko da me Kotun Koli ta bayar, ba za a amince da wasu ba.
“A batun Ojukwu da gwamnatin jihar Legas, da zarar jama’a masu tunani sun koma gida suna ganin cewa bangaren shari’a na nuna son kai, to ya karya manufar da aka kafa bangaren shari’a. Kiranmu ga alkalan mu shi ne su yanke hukuncin da zai sa ‘yan kasa su amince da bangaren shari’a.
A wani labarin kuma:Har yanzu kuɗaɗen gudanarwa su ne babban kalubale a jami’o’i – Shugabannin Jami’o’i
Kwamitin shugabannin jami’o’in Najeriya, CVCNU, ya bayyana rashin isassun kudade a matsayin daya daga cikin manyan kalubalen da ke yaki da ci gaba mai inganci da martabar jami’o’in gwamnati a Najeriya.
Sakatare-Janar na CVCNU, Farfesa Yakubu Ochefu, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a Abuja a wani taron karawa juna sani na ci gaba da jami’an tsofaffin dalibai suka shirya.