Wakilinmu Mu’azzam Yakubu Sanka
Daga Lokacin da na Shigo Wannan Hukumar mun yi Kes ya fi Dubu Hudu, kuma mafi yawa daga cikin su Marasa Karfi Muke Taimaka, wasu ma mu muke uwa kuma muyi makarbiya.
Domin yana daga aikin Wannan Hukumar Yaki da Al’mundahana da cin hanci da Rashawa Karbar Korafe-Korafe daga ko’Ina da Zurfafa Ingantaccen Bincike gami da daukar Matakin Shari’a.
Shugaban Hukumar ta Kasa Reshen Jihar Kano Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya Ce aikin Wannan Hukuma ya Shafi binkice da Tsatsefe Bayanai domin yiwa kowa Adalci.
Wannan Yasa Duk lokacin da Wani Korafi yazo gabanmu muke neman abokin maganar domin shi ma muji ta bakin sa kafin daukar wani mataki Nagaba, inji shi.
Kuma a duk tsawon wannan lokacin da muke wannan fafutuka babu kes din da wasu suka dage ala dole sai sun Hana cigaba da yin binkicen irin na Masarauta.
Kuma abin mamaki masu kokarin kawo mana cikas a Binkicen ba cewa suke yi ba a aikata laifin ba, ko kuma Hujjojin da muke dauke da su Kirkirar su muka yi ko kuma karya ne ba, kawai dai sun dage ne sai sun kawo ma Binkicen Tasgaro, ko meye dalilin su.
Dan haka Wannan Hukuma ta Public Complaints and Anti Corraption Commission, tana Iya Kokarinta wajen yi ma Kowa Adalci kuma duk binkicen da ke Gabanta tana nan tana yin sa kamar Yadda doka ta tanada sannan da zaran mun kammala binkice za Ku ji matakin mu na gaba.