Shugaba Bola Tinubu, a daren ranar Laraba, ya tabbatar wa shugabannin kungiyar kwadago cewa matatar mai ta Fatakwal za ta fara aiki nan da watan Disambar 2023, kamar yadda Punch ta rawaito.
Kungiyar kwadagon ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar a daren ranar Laraba.
KARANTA WANNAN: Taleko ta Koma: Majalisar Dokokin Wata Jiha Ta Ki Amincewa Da Nadin Wata Kwamishiniya
Cibiyoyin kwadagon sun kuma lura da cewa shugaban ya yi alkawurra da dama inda suka amince da komawa kan teburin tattaunawa.
Shuwagabannin kungiyar kwadago ta kasa, Joe Ajaero da TUC, Festus Osifo a cikin sanarwar sun kuma yabawa ‘yan Najeriya kan goyon bayan zanga-zangar da aka gudanar a fadin kasar.
“Ya dace a sanar da ‘yan Najeriya cewa girman nasarar da zanga-zangar ta yi wanda aka jadada bisa bukatar shugaban tarayyar Najeriya; Sanata Ahmed Bola Tinubu zai gana da shugabannin NLC da TUC a wani zama na sirri.
“Haɗin gwiwar ya yi amfani sosai, an samu gaggarumin tafiyar da ya shafi al’amuran da suka dabaibaye ayyukan kwamitin shugaban ƙasa kan cire tallafin da ya sa aka yi zanga-zangar; Ya himmatu wajen sake fasalin tsarin aiki cikin gaggawa daidai da shigar da shugabannin kwadago.
“Ya ba da tabbacin cewa matatar mai ta Fatakwal za ta fara aiki a watan Disamba na wannan shekara. Ya yi alkawarin tabbatar da ganin an cimma yarjejeniya kan bayar da kyautar albashi ga ma’aikatan Najeriya nan take.
“Ya yi alƙawarin buɗe taswirar hanya mai aiki zuwa madadin CNG mako mai zuwa. A bisa ƙarfin alkawari da jajircewar shugaban ƙasa, mun yanke shawarar komawa sabon tsarin tattaunawa don ba da damar aiwatar da cikakken aiki.
“Muna kara godiya ga ‘yan Najeriya yayin da muke jiran gwamnati ta cika nata bangaren fahimtar kamar yadda aka amince da shugaban kasa.”
A wani labarin kuma, Gwamnan PDP Ya Kaddamar da Shugabannin Riko Na Kananan Hukumomi 20
Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed na jihar Bauchi a ranar laraba ya kaddamar da sabbin shugabannin kwamitocin riko na kananan hukumomi 20 da mataimakansu.
Gwamnan ya hore su da su guji cin hanci da rashawa, maimakon haka su kasance masu gaskiya da rikon amana wajen gudanar da ayyukansu.