Da Ɗumi-Ɗuminsa: Kotun daukaka kara ta tabbatar da Mbah a matsayin Gwamnan Enugu
Kotun sauraren kararrakin zabe da ke zamanta a jihar Enugu, a ranar Alhamis, ta tabbatar da zaben gwamna Peter Mbah na jam’iyyar PDP.
DAILY POST ta rahoto cewa an ƙalubalanci zaben Mbah wanda Barr Chijioke Edeoga na Jam’iyyar Labour, LP ya yi.
KARANTA WANNAN LABARIN:Hukuncin zaben Gwamna a Kano rashin adalci ne, Shugaban SDP
Manyan dalilan da ya sa Edeoga ya shigar da kara sun ta’allaka ne kan zargin Mbah na jabun takardar masu yi wa kasa hidima, NYSC, wasu kura-kurai a lokacin zabe, yawan kuri’u da sauransu.
Shugaban kwamitin mutane uku, Mai shari’a Kudirat Morayo Akano ya yi watsi da karar inda ya amince da wanda ake kara Mbah.
Ya soke bukatar Edeoga na neman a haramtawa Mbah cancantar shiga takara bisa zargin yin jabun takardar shaidar NYSC.
Kwamitin ya ce takardar shaidar NYSC kamar yadda sashe na 177 na kundin tsarin mulkin kasar na shekarar 1999 ba shi ne abin da ake bukata na tsayawa takarar gwamna ba.
An yanke hukuncin cewa Mbah bai mika wa INEC satifiket din sa na NYSC ba domin ya samu damar tsayawa takarar gwamna, tunda ya riga ya cancanta ba tare da takardar shaidar yi wa kasa hidima ta NYSC ba.
Hakazalika kotun ta yi watsi da zarge-zargen wuce gona da iri da kuma yin watsi da BVAS.
Kwamitin ya kuma ce shaidun da jam’iyyar Labour ta gabatar ba wakilai ne da INEC ta amince da su ba, kuma shaidarsu ba ta da tushe.
An tabbatar da cewa an zabi Mbah a matsayin gwamna da mafi rinjayen kuri’un da aka kada a lokacin zaben.
Har ila yau, tun a ranar ta yi watsi da karar da jam’iyyar People’s Redemption Party, PRP, dan takarar gwamna, Elder Christopher Agu, ya shigar.
A wani labarin kuma:NUJ ta yi Allah wadai da rasuwar wakilin VON a Zamfara
Kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya, NUJ, ta bayyana damuwarta kan rasuwar wani mamba a garin Gusau na jihar Zamfara, Hamisu Danjibga.
Kungiyar ta yi kira ga ‘yan sanda da su tona asirin waɗanda suka yi sanadiyyar mutuwarsa.