A ranar Juma’a ne wasu mutane da suka hada da ‘yan majalisar dokokin Benue biyu da magoya bayan jam’iyyar PDP a cikin ayarin motocin gwamnan jihar, Samuel Ortom, suka yi hatsari a unguwar Utokon, yayin da suke rangadin yakin neman zabe a karamar hukumar Ado ta jihar.
Dogayen ayarin magoya bayan jam’iyyar PDP karkashin jagorancin gwamna Samuel Ortom sun kasance a gundumar Benuwe ta Kudu a ci gaba da gangamin yakin neman zaben gwamnan jam’iyyar a lokacin da hatsarin ya afku.
KARANTA WANNAN LABARIN: Da Dumi-dumi: Kwamandan Amotekun Ya Yi Murabus daga Matsayin Sa
Wakilinmu ya rawaito cewa lamarin ya faru ne a lokacin da direban wata motar bas cike da magoya bayan jam’iyyar PDP ya yi kasa a gwiwa inda ya bugi motoci uku; Jeep, motar jami’an tsaro da wata bas a cikin ayarin motocin.
Magoya bayan jam’iyyar da dama da suka hada da ‘yan majalisar dokokin jihar mai wakiltar Guma da Kwande ta yamma a majalisar dokokin jihar sun jikkata a hadarin da ya afku da misalin karfe 10:50 na safiyar ranar Juma’a wanda kuma ya shafi wasu motoci.
Motocin da ke cikin ayarin sun hada da mataimakin gwamnan jihar, Injiniya Benson Abounu, Sanata Abba Moro, ‘yan majalisar wakilai da majalisar dokoki daga gundumar Benue ta kudu da sauran manyan jami’an gwamnati da na jam’iyyar a jihar.
A halin da ake ciki, motar daukar marasa lafiya da ke cikin ayarin motocin ta kwashe wadanda suka jikkata zuwa asibiti yayin da sauran suka ci gaba da tafiya.
A wani labarin kuma, Yanzu-yanzu: Kotu Ta Dakatar Da Umarnin Gwanjon Kadarorin Ekweremadu
Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi watsi da umarnin wucin gadi na kwace kadarorin tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa, Ike Ekweremadu.
Da yake yanke hukunci a ranar Juma’a, alkalin kotun Inyang Ekwo, ya ce hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta boye gaskiya lokacin da ta nemi a kwace kadarorin na wucin gadi.