- Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya yi alfahari da kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da makwabciyar kasar Nijar.
- Shugaban ya bayyana haka ne a yayin kaddamar da hedikwatar hukumar kwastam ta Najeriya kan naira biliyan 19.6 a Abuja,
- Buhari yace “Idan wani mai karfi ya motsa, yana da kyakkyawar alaka da makwabtansa mutanen Nijar za su kare shi.”
Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya yi alfahari da kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da makwabciyar kasar Jamhuriyar Nijar,Punch ta rawaito.
Buhari, wanda wa’adinsa zai kare nan da kwanaki shida, ya danganta amincewar da ya yi na tsaron kasar da kyakkyawar alaka da yake da ita Nijar.
KARANTA WANNAN LABARIN: Da Dumi-Dumi: An Saki Wamakin Daya Dallawa Jami’in Dan Sanda Mari
Ya ce idan rayuwa ta yiwa ‘yan Najeriya wahala bayan bikin mika mulki da aka shirya yi a ranar 29 ga watan Mayu, Nijar za ta taimaka masa.
Shugaban ya bayyana haka ne a yayin kaddamar da hedikwatar hukumar kwastam ta Najeriya kan naira biliyan 19.6 a Abuja, ranar Talata.
Shugaba Buhari, yayin jawabinsa a bikin kaddamarwar, ya kuma bayyana cewa yana shirin komawa jiharsa ta Daura, mai nisa da Abuja, kuma kusa da Jamhuriyar Nijar.
Ya ce, “Na faɗi waɗannan ƴan abubuwan game da imanina domin saura kwanaki shida kawai na tafi.
“Kuma na yi kokarin yin nisa da Abuja yadda ya kamata. Na fito daga wani yanki mai nisa da Abuja.
“Na ce idan wani mai karfi ya motsa, ina da kyakkyawar alaka da makwabtana mutanen Nijar za su kare ni.”
A cewarsa, idan mutum ya kasa samun amincewar makwabcinsa, shi ko jikansa za su shiga cikin matsala.
Buhari ya kuma bayyana cewa da gangan ya nada mata a matsayin ministocin kudi a cikin shekaru takwas da ya yi yana mulki domin yakar tashe-tashen hankula daga mutanen da ke neman bayar da kwangila da biyan kudaden kwangila.
Shugaban ya yi nuni da cewa kwarjinin mafi yawan maza za su tsaya musu ne domin neman alfarma daga mace a matsayin ministar kudi.
JARIDAR DIMOKURADIYYA ta rawaito cewa ministar kudi ta farko a mulkin Buhari ita ce Mrs.Kemi Adeosun, wacce ta yi murabus bayan badakalar NYSC a shekarar 2017.
Bayan murabus din Adeosun, shugaban kasar ya nada Mrs. Zainab Ahmed, shugabar ma’aikatar kudi.
Ya ce, “Da gangan na nada mata don ya ba ni kwanciyar hankali.
“Na tabbatar da na baiwa wata mata ma’aikatar kudi domin ta yi amfani da dabi’ar al’adun ‘yan Najeriya baki daya: da zarar mata sun rike mukamin, mutane suna jin girman kai ga mata.
“Don haka, na tabbata za a ba da zaman lafiya a ma’aikatar kudi, inda mutane za su je su ba da kwangilar a biya su, da sauransu. Don haka, suna jin girma wajen kwantar da kai da yawa ba za su je wurin matan ba.”
A wani labarin kuma, Da Dumi-Dumi: CBN Ya Soke Lasisin Wasu Bankuna 132
Babban bankin Najeriya CBN ya kwace lasisin gudanar da ayyukan wasu bankunan Microfinance guda 132 da sauran wuraren hada-hadar kudi.
Bankunan sun kasa yin aiki da wajibcin da babban bankin Nijeriya ya dora musu bisa tanadin dokar Bankunan da sauran cibiyoyin hada-hadar kudi BOFIA