Daruruwan ‘yan kungiyar Kwankwasiyya ne suka hallara a Kano a ranar Alhamis domin gudanar da addu’o’i na musamman domin samun nasarar Gwamna Abba Kabir Yusuf a kotun sauraron kararrakin zaben Gwamna.
Jam’iyyar adawa ta APC na kalubalantar nasarar da Yusuf na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP ya samu a zaben gwamnan jihar Kano da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.
KARANTA NANTinubu Zai Mayar Da Hankali Wajen Bunkasa Fannin Lafiya A Najeriya-Gwamnatin Tarayya
Sai dai a yayin da kotun ke shirin yanke hukunci kan rikicin zaben gwamna, ‘yan Kwankwasiyya na neman sa hannun Allah.
Sallar wacce ta kunshi maza da mata mabiyan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Rabi’u Musa Kwankwaso, an gudanar da addu’o’in ne a titin Zaria, Maiduguri, Hadejia da Gwarzo wadanda su ne manyan hanyoyin shiga birnin na dabo ba gari ba dajin Allah
Da take jawabi a daya daga cikin wuraren addu’o’in, shugabar kungiyar mata ta NNPP ta jihar, Hajia Zuwaira Abubakar, ta yi ishara da cewa suna addu’a ga wadanda suke da niyyar tsige Yusuf a matsayin gwamnan jihar Kano.
Ta ce muna sane da irin yadda aka yi kaurin suna da aikata laifuka a karkashin kasa domin kwace nasarar da gwamnatin NNPP ta yi mana a jihar Kano da kuma rokon Allah da ya dauki nauyin masu wannan yunkuri.
A WANI LABARIN KUMAMuna Iyakar Kokarinmu Wajen Dawo Da Wutar Nepa A Wasu Yankunan Najeriya-Ministan Lantarki
Abubakar ta bayyana cewa ba za su bari wasu da ba su ji dadi su dauke nasarar Yusuf a zaben gwamna.
Ta bayyana nasarar da gwamnan ya samu a zaben a matsayin farin jini domin kuwa dukkan kanawa sun fito ranar zabe sun nuna cewar suna tare da Abba Kabir Yusuf kuma suna tare da jagoran kwankwasiyya Rabiu Musa inji Zuwaira.
Ya Allah kabaiwa me girma gwamna jihar kano engr.abba kabir yusif nasara a kotun sauraren karararrakin zabe da ke kano kamar yadda ka bashi nasara a zaben daya gabata katabbatar masa da kujerarsa.