Shahararren Mai Rajin kare hakkin Bil’adama din nan, kuma shugaban ‘kungiyar Concerned Nigerians, wato Deji Adeyanju ya yi tir da Allah-wadai da wadanda suka sace ‘ya’yan Musulmi a Kano, suka sauya halittarsu da maishe su Kiristoci, suka siyar da su a garin Anambra.
Deji Adeyanju ya ce; akwai bukatar a yi bincike a kuma hukunta wadanda suke da hannu a ciki.
Deji ya wallafa hakan ne a shafinsa na Twitter da Facebook.