Adams Oshiomole, shugaban jami’iyyar APC na kasa yace ‘yayan jami’iyyar APC ne kadai zasuyi shugabancin kwamiti a majalissar tarrayar a cikin wannan zangon da za’a shiga.
Oshiomhole ya bayyana haka ne a taron ganawa da shugaban Kasa Muhammadu Buhari yayi da zababbun ‘yan majalisar Tarayya na jam’iyyar APC a fadar gwamnati ranar Talata.
Mun tafka kuskure a shekarar 2015 wajen zabe shuwagabanni, amma yanzu bazamu yadda muyi kuskure ba. ‘Yan jami’iyyar mune kawai zasu rike manyan mukamai a majalisa.