By Abbas Yakubu Yaura
Fadar Shugaban kasa ta zargi wasu Gwamnonin Najeriya da kai wa Shugaban kasa Muhammadu Buhari hari da gangan don kawar da hankalin ma’aikatan gwamnatinsu daga biyan albashi da fansho duk wata.
Femi Adesina, babban mataimaki na musamman ga shugaba Buhari kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, wanda ya yi wannan zargin a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis a Abuja, ya ce gwamnonin na dora laifin duk wani mummunan abu a jihar su ga shugaba Buhari.
A cewarsa, wasu daga cikin gwamnonin da suka yi fice wajen yin adawa da shugaban kasar, ba su da wata hanya ta kilomita daya a jihohinsu da gwamnatinsu ta gina.
Adesina ya bayyana cewa, duk da yunkurin da suka yi na rufe gazawarsu wajen biyan albashi da samar da ababen more rayuwa, har yanzu al’ummar Jihohinsu na rike da su, yana mai jaddada cewa ‘yan kasar sun san inda matsalolinsu ke fitowa.
Ya ce, “Wasu Gwamnonin suna ganin za su iya zama jarumai ta hanyar yi wa Shugaban kasa gaba. Idan suna bin albashi da fansho, da zarar watan ya kare, sai su fara zagin Shugaban kasa, suna tunanin jama’arsu za su manta da albashi da fansho da ba a biya ba. Da ba su yi titin kilomita daya ba, Buhari ne.
“Lokacin da kayayyakin more rayuwa suka lalace a karkashinsu, Buhari ne. Lokacin da ba za su iya kare rayuka da dukiyoyin al’ummar da suke mulki ba, Buhari ne.
“Suna wasa zuwa gidan kallo, suna tunanin za su sami yabo daga mutanensu. A’a, kawai sautin da mutane ke ji, shi ne ruhohin cikkunansu, saboda yunwa. Kuma sun san daga ina matsalarsu ta fito”.