Kylian Mbappe ya ce Faransa mai rike da kofin duniya za ta je wasan karshe na gasar cin kofin duniya na badi don lashe gasar bayan ya ci kwallaye hudu a ragar Kazakhstan da tayi rashin nasara da ci 8-0 a hannun Faransa, wanda ya tabbatar da cancantar shiga gasar na Kofin Duniya.
Dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint-Germain Mbappe ya ci kwallon farko a wasan daf da na kusa dana karshe a ranar Asabar, abin da ya sa ya zama dan wasan Faransa na farko da ya taba samun wannan matsayi a gasar cin kofin duniya tun bayan Dominique Rocheteau a shekarar 1985.
Ya kara da na hudu a karshen wasan inda Faransa ta sami tikitin zuwa Qatar a filin wasa na Parc des Princes dauke da tutoci ja, fari da shudi.
“Abu mafi mahimmanci shine cancanta saboda muna son ba kanmu damar kare kambun mu.
KARANTA WANNAN LABARIN: Yan sanda Sun Kama matsafa da kan Mutum a Ogun
“Kofin Duniya mafarki ne, manufa, komai ne kuma dama ce ta musamman ta taka leda a kungiyar da za ta iya lashe ta. Za mu je can don mu ci nasara.”