Kimanin sa’o’i 48 kafin gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya, jam’iyyar PDP da Labour ta rasa mambobin jam’iyyar zuwa APC da dama a babban birnin tarayya Abuja.
Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya rawaito cewa an tarbi wadanda suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC ne a ranar Laraba a Abuja.
KARANTA WANNAN LABARIN: Rundunar Yan Sandan Kano Ta Bukaci Kwankwaso Ya Dage Yakin Neman Zabensa A Jihar
Ko-odinetar National Mass Movement for Better Orientation ta kasa, Dakta Hawa Iyatu-Bagu, wata kungiya mai goyon bayan Tinubu, ta ce ci gaban da aka samu alama ce ta nasarar da APC zata samu a zaben da za a yi a ranar 25 ga watan Fabrairu.
Iyatu-Bagu ta ce kungiyar ta dade tana tuntubar wadanda suka sauya sheka, inda ta ce, “a yau wadanda suka amince da gaskiya sun yanke shawarar bin kungiyar da ta yi nasara.
Ta ce, “Mun yi ta zagayawa don neman kuri’u kuma galibinsu a nan shugabanni ne kawai domin idan dukkansu za su kasance a nan, wannan wurin ba zai iya dauke su ba.
“Don haka, yanzu muna rokon shugabanninsu da wasunsu da su zo nan su bayyana wa jama’a shawararsu na ficewa daga PDP da LP su bayyana a shirye su ke su zabi Tinubu da Shettima.
“Da wannan ci gaban da kuma abin da muka gani ya zuwa yanzu a yayin yakin neman zabe a ko’ina cikin Najeriya, ‘yan Najeriya, musamman mata a shirye suke su zabi ‘yan biyu.”
Ko’odinetan ta kuma bayyana cewa matasan sun shirya tsaf domin tabbatar da nasarar Tinubu, inda ta tabbatar wa wadanda suka sauya sheka cewa za a yi musu adalci daidai wa daida.
A cewarta, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC zai mayar musu da duk wani mataki da za a yi musu da ingantaccen shugabanci.
Shima da yake nasa jawabin mataimakin ko-odinetan NAMMBO na kasa Ibrahim Umar ya yabawa kungiyar goyon bayan Tinubu kan jawo wadanda suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.
Umar, ya ce wannan damace da Tinubu ya samu na lashe zaben shugaban kasa na da matukar haske, inda ya kara da cewa ‘yan Najeriya sun yi sha’awar zaben Tinubu da Shettima.
Tun da farko, Mista Titus Musa, tsohon shugaban matasan jam’iyyar PDP a unguwar Gwarinpa, karamar hukumar Abuja, wanda ya jagoranci masu sauya shekar ya ce sun yanke shawarar sauya sheka zuwa APC ne domin zaben Tinubu.
Ya ce, “Wannan ya samo asali ne saboda kyawawan ayyukan da ya yi a Legas da kuma gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban kasa.
“Mun gamsu da tsarin jam’iyyar APC mai taken saƙon bege. APC ce hanyar da za ta bi kuma Tinubu yana da abin da zai ba Najeriya.
A nata bangaren, tsohuwar shugabar matan jam’iyyar Labour Party a unguwar Gwarinpa, Ms Zipporah Bitrus, ta bayyana cewa sun bar LP zuwa APC ne kasancewar Tinubu da Shettima ne suka fi dacewa da kasar nan.
“Tinubu mutum ne da a kodayaushe ya damu da inganta rayuwar talakawa.
“Ya shawarci ‘yan Najeriya da dama kuma shi ya sa muke ganin dalilan da suka sa muka kafa tantinmu da APC.NAN
A wani labarin kuma, Wata Radiyo Ta Fasa Hira da Dan Takarar Gwamna Bayan Ya zauna Domin Gabatar Da Shirin
Jam’iyyar PDP a jihar Ogun ta zargi jam’iyyar APC mai mulki da yaudarar ‘yan jaridu a kokarinta na hana jin muryoyin ‘yan adawa.
PDP ta yi zargin cewa jam’iyyar APC da gwamnatinta sun ci gaba da hana kafafen yada labarai su rika yada ayyukanta na rashin son zuciya saboda gwamnati ba ta son a rika suka.