Gwamnan jihar Adamawa Ahmadu Fintiri a ranar Juma’a ya gabatar da kudirin kasafin kudi na Naira biliyan 175 ga majalisar dokokin jihar domin tantancewa a matsayin kasafin kudin jihar na shekarar 2023.
Da yake gabatar da kasafin kudin ga ’yan majalissar a zauren majalissar a Yola, Fintiri ya ce ya sanya wa kasafin kudin hadin gwiwa da ayyukan da za za su hada da abubuwan da gwamnatinsa ta yi a shekaru masu daraja tun da ya zama gwamna a shekarar 2019.
KARANTA WANNAN LABARIN:
Jami’an ‘Yan Sanda Sun Cafke Wasu Jami’an EFCC Na Bogi
A cewarsa, jimillar kudirin kasafin kudin na Naira biliyan 175,019,054,060 ya kunshi kudirin kashe kudade akai-akai na Naira biliyan 105,011,432,436 ko kashi 60 cikin 100 na abin da aka gabatar, da kuma kudirin kashe kudi na Naira biliysn 70,007,621624 ko kuma kashi 40 na adadin kasafin kudin.
Ya sanar da cewa, an ware kaso mafi girma na ilimi a cikin kudirin kashe kudi domin baya ga yin aiki don ci gaba da gudanar da ayyuka da dama a bangaren wasu sabbi ayyuka, kamar kafa makarantu na musamman guda uku na masu hazaka, za a ware musu daga cikin kasafin kudin da aka tsara.
A cikin dogon jawabinsa na kasafin kudi, ya yi alkawarin cewa, bisa ga al’adarsa na gaggauta aiwatar da ayyuka, za a kammala dukkan ayyukan da ake gudanarwa cikin wa’adin da aka ba su.
Da yake mayar da martani ga jawabin gwamnan, kakakin majalisar dokokin jihar Adamawa, Rt Hon Aminu Iya Abbas, ya bayyana kwarin gwiwar cewa idan aka duba aka kuma amince da kasafin kudin shekarar 2023, majalisar ministocin Fintiri za ta aiwatar da shi cikin himma.
Ya sanar da cewa, bisa gamsuwa da yadda Fintiri yake aiwatar da shirin bayar da ilimi kyauta ga ‘yan jihar, Majalisar ta fara aiki da wani kudiri na samar da dokar da ta tilasta wa dukkanin gwamnonin da suka biyo baya su aiwatar da ilimin matakin farko kyauta kuma wajibi a jihar.
A wani labarin kuma, Yanzu-Yanzu: Kotu Ta Soke Dukkan Zaben Kananan Hukumomi Jihar Osun
Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Osogbo, babban birnin jihar Osun a ranar Juma’a, ta soke zaben kananan hukumomi da hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Osun ta gudanar a ranar 15 ga watan Oktoban da ya gabata.
Mai shari’a Nathaniel Ayo-Emmanuel, a hukuncin da ya yanke, ya ce zaben da aka gudanar ya sabawa tanadin sashe na 29 da 32 na dokar zabe ta 2022.