Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya yi kira ga hukumar shirya jarabawar kammala sakandire ta Najeriya (WAEC) da ta dauki matakin rage yawaitar tabarbarewar jarabawa.
Sule ya bayyana haka ne a ranar Alhamis a Lafiya a taron shekara-shekara na NNC na WAEC karo na 61.
Karanta nanHukuncin Kotun Koli Ba Zai Sanyaya Mana Gwuiwa Ba–Gwamnatin Zamfara
Ya lura cewa don kawar da yawaitar satar amsa akwai bukatar a kara kaimi wajen dakile hakan.
Ya ce, domin kare makomar yara da kuma makomar kasa baki daya, akwai bukatar a gaggauta magance matsalar satar jarabawa domin ta kasance babbar matsala ga harkar ilimi.
Ilimi zai kasance har abada gadon gadon gado ga yara da matasa na Jihar Nasarawa musamman, kuma shine kawai ingantaccen kayan aiki na ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin jihar da kasa baki daya.
Hakika na yi farin cikin lura da cewa duk da dimbin kalubalen da ke addabar fannin ilimi a Najeriya, majalisar ta ci gaba da zama wata alama ta samun nasara wajen inganta ilimi mai inganci.
A wani labarin kumaAn Rasa Rai,Yayinda ‘Yan Shia Suka Yi Arangama Da ‘Yan Sanda A Kaduna
Hakika gwamnatinmu tana kokari matuka wajen samar da ingantaccen tushe mai dorewa a fannin ilimi, ta hanyar samar da ilimi mai inganci da rahusa ga matasa tare da magance kalubalen da yara masu bukata ta musamman ke fuskanta a jiharmu.” Inji shi.
Gwamnan ya bayyana cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da samar da yanayi da zai karfafa koyo ga dalibai a makarantun gaba da sakandare na jihar.
Ya kuma bukaci iyaye da su ba da himma wajen bunkasa ilimi a ‘ya’yansu.