- Gwamnan Borno Babagana Umara Zulum ya amince da fitar da naira miliyan 10 a matsayin tallafi ga sojojin da suka samu raunuka
- Tallafin dai ya kasance cika alkawari ne da Gwamnan ya yi watanni biyu da suka gabata a wajen bikin Sallah wanda babban hafsan sojin kasa ya shirya
- Sojojin sun sha alwashin kawar da ragowar masu tada kayar baya da ke dagewa a yakin
Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya amince da fitar da naira miliyan 10 a matsayin tallafi ga sojojin da suka samu raunuka a fadan da aka gwabza a Borno.
Tallafin dai ya kasance cika alkawari ne da Gwamna Zulum ya yi watanni biyu da suka gabata a wajen bikin Sallah wanda babban hafsan sojin kasa, Manjo Janar Taoreed Lagbaja ya shirya.
KARANTA WANNAN: Nasarawa: PDP ta Koka da Murdiyar Shari’ar Kotu da APC ta Yi
Kwamishinan yada labarai da tsaron cikin gida na jihar Borno, Farfesa Usman A Tar, tare da rakiyar babban sakatare na gidan gwamnati, Barista Mustapha Ali Busuguma, sun kai wa runduna ta 7 ta GOC ta sojojin Najeriya, Manjo Janar Peter Malla kyautar gwamnmnatin, a dakin taro na 7 Division a hedkwatar Maiduguri a ranar Asabar, 19 ga watan Agusta 2023.
“Mun zo nan ne domin cika alkawarin da mai girma Gwamnan Jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum ya yi.
“Za ku iya tuna cewa Gwamnan ya zo ne a ranar Sallah domin wani biki, inda ya bayyana kudirin gwamnatin jihar Borno kan jin dadin dakarun mu tare da bayar da gudunmuwar Naira miliyan 10 ga sojojin da suka jikkata.” Inji Farfesa Tar.
Gwamnan ya kuma bayyana kudurinsa na ci gaba da bayar da goyon baya wajen baiwa Gwamnatin Tarayya tallafin kayan aiki da inganta walwalar sojoji. Ya kuma yabawa sojoji kan kare martabar yankin Najeriya da kuma tabbatar da zaman lafiya a Borno.
Da yake karbar tallafin, runduna ta 7 ta GOC, Manjo Janar Peter Malla ya nuna jin dadinsa ga Gwamna Zulum bisa wannan karimcin.
“Bari ni a madadin Kwamandan ina maraba da ku zuwa runduna ta 7 Division kuma ina so in nuna godiyarmu ga mai girma Gwamna kan yadda yake tallafa wa sojoji a koyaushe,” in ji Manjo Janar Malla.
GOC ya ba da tabbacin dorewar zaman lafiya da ake samu a Borno ta hanyar kawar da ragowar masu tada kayar baya da ke dagewa a yaki.
A wani labarin kuma, Yobe: Gwamna Buni ya Rantsar da ‘Yan majalisar zartaswa, Ya Nemi Wata Bukata
Gwamnan Yobe, Mai Mala Buni ya rantsar da Kwamishinoni guda 20
Gwamnan yace akwai bukatar su himmantu wajen aiki tukuru, su kasance masu biyayya ga Gwamnatin jihar
Gwamnati na ba zata yadda da babakere ko sama da fadi ba, ko kuma rashin kwazo a yayin gudanar da aiki
Gwamnan Jihar Yobe, Alhaji Mai Mala Buni ya rantsar da Kwamishinoni guda 20.
JARIDAR DIMOKURADIYYA ta rawaito cewa bikin rantsarwar ya gudana ne a dakin taro da ake kira Banquet Hall dake fadar Gwamnati a Birnin Damaturu.