Gwamnatin na kashe N8.3trn akan jami’anta, amma abun baƙin ciki ba za ta iya baiwa ASUU N1trn ba – Ndume
Sanata Ali Ndume ya soki gwamnatin Najeriya kan ware tiriliyan nairori ga jami’an gwamnati.
Ndume yana son kashi 50 cikin 100 na albashin ‘yan majalisar tarayya da ake warewa kungiyar malaman jami’o’i (ASUU).
KARANTA WANNAN LABARIN: Shekarar 2023 zata kasance lokaci mai tsanani ga ƴan Najeriya — Shettima ga Ƴan Najeriya
A ranar Alhamis ne dan majalisar dokokin Borno ta Kudu ya mayar da martani kan rabin albashin da malaman suka biya.
Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan ya lura cewa ’yan majalisar na taruwa sau biyu a cikin mako mafi yawan lokaci kuma suna samun albashi.
“Ko da hakan na nufin Majalisar Tarayya za ta rage alawus-alawus din zama ko kuma a biya kan kwanakin aikin da mutum yayi”, NAN ta ruwaito.
Ndume ya ce Najeriya ta kashe tiriliyan 20.5 a shekarar 2023 amma ba za ta iya baiwa ASUU Naira tiriliyan 1 ba don magance kalubalen da ke addabar fannin ilimi.
Dan siyasar ya ci gaba da korafin cewa an tilasta wa dalibai zama a gida tsawon watanni takwas ba su yi komai ba.
“Idan za ku iya kashe Naira Tiriliyan 8.3 kan ma’aikatan gwamnati, me ya sa ba ku kashe N1trillion a jami’o’in gwamnati?” Ya tambaya
A wani labarin kuma: 2023: Ku Zaɓi Duk Wanda Kuke So, Buhari Ga Ƴan Nijeriya
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce ‘yan Najeriya su zabi wanda suka ga dama daga kowace jam’iyyar siyasa a lokacin zaben 2023.
Ya ce ba za a bari wani ya tara dukiya da ‘yan daba domin tsoratar da jama’a a kowace mazaba.