Gwamnatin Tarayya Na Neman Masu Cutar Ƙanjamau 280,867
Gwamnatin tarayya ta ce tana aiki tare da hadin gwiwa da masu ruwa da tsaki da kuma abokan hulda domin kawo mutane 270,000 da ke dauke da cutar kanjamau domin karɓar magani.
Jami’in kula da shirin yaki da cutar kanjamau na kasa (NASCP), Dakta Adebola Bashorun ya bayyana haka a Legas a wajen bude taron kwana biyu na yaki da cutar kanjamau na kasa (DPR).
KARANTA WANNAN LABARIN:Yadda Wasu Ƴan Majalisa Suka Gana Da Ganduje Kan APCn Oyo
Daily Trust ta ruwaito cewa an kiyasta ‘yan Najeriya miliyan 1.9 na dauke da cutar kanjamau yayin da 1,630,000 ke karbar magani.
Bashorun ya ce Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa (DSD) ta inganta ingancin kulawa da ake bai wa al’ummar da ke dauke da cutar kanjamau.
A wani labarin kuma:Gwamnan Kano Ya Sake Yin Sabbin Naɗe-Naɗe 20
Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da daukaka matsayin mai magana da yawunsa, Sanusi Bature Dawakin Tofa, daga babban sakataren yada labarai na babban daraktan yada labarai
Gwamnan ya kuma amince da nadin karin shugabannin hukumomi bakwai da masu ba da shawara na musamman 13.