Hukumar NPFL ta ci tarar Kano Pillars, Gombe United saboda rashin da’a
Hukumar kula da kwallon kafa ta Najeriya NPFL ta ci tarar Kano Pillars da Gombe United sakamakon rashin da’ar da magoya bayansu suka yi a wasan da suka yi da Plateau United ranar Lahadi.
Magoya bayan Pillars ne suka kawo tarnaki kai tsaye a wasannin da aka yi a filin wasa na Sani Abacha.
KARANTA WANNAN LABARIN:Hukumar Hisbah Ta Lalata Kwalaben Barasa 850 a Katsina
An ci tarar Naira miliyan 10 ga kulob din saboda rashin da’a da magoya bayansu suka yi.
Kano Pillars za ta biya tarar Naira miliyan 1 kan laifin jefa abubuwa da dama a fili da kuma wasu Naira miliyan 1 kan rashin da’a da za ta iya kawo wa wasan kunya.
Za a biya tarar N250,000, zama diyya, ga mataimakin alkalin wasa Sodiq Adejumo kan raunin da ya samu.
Kano Pillars za ta buga wasanta na gaba a gida a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano kafin a tafi hutun rabin lokaci ba tare da magoya baya ba.
Hakazalika, ita ma Gombe United an ci tarar Naira miliyan 3.75 saboda tabarbarewar tsaro a wasansu da Rivers United.
An dakatar da babban kociyan kungiyar kwallon kafa ta Gombe United Mohammed Baba Ganaru daga kan kujeran fasaha na kungiyar na wasanni uku masu zuwa.
Kungiyar kwallon kafa ta Gombe United ma ta samu maki uku da kwallaye uku a ragar da suka tara sakamakon cin zarafin jami’an wasan.
Savannah Scorpions kuma za su buga wasansu na gaba na gida a filin wasa na Pantami ba tare da magoya baya ba kafin hutun tsakiyar kakar wasa.